Saturday, December 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ba gayyar sodi tasa na aika sojoji kasar Benin Republic ba, rokona suka yi>>Fadar Shugaba Tinubu

Ba gayyar sodi tasa na aika sojoji kasar Benin Republic ba, rokona suka yi>>Fadar Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Fadar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa, ba haka kawai gayyar sodi tasa shugaban kasar ya aika da sojoji kasar Benin Republic ba. Yace kasar ta Benin Republic ce ta bukaci hakan. Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Bayo Onanuga. Hakan na zuwane jim kadan bayan da shugaban ya aikawa majalisar Dattijai bukatar aikawa da sojoji kasar Benin Republic inda kuma suka amince.
Da Duminsa: ECOWAS ta saka dokar ta baci a Afrika ta yamma saboda yawaitar Jhuyin mulki

Da Duminsa: ECOWAS ta saka dokar ta baci a Afrika ta yamma saboda yawaitar Jhuyin mulki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar Hadin kan kasashen Afrika ta yamma, ECOWAS ta saka dokar ta baci saboda yawaitar juyin mulki a kasashen Yankin Shugaban kungiyar, Omar Touray ne ya bayyana hakan a taron kungiyar da aka yi a babban birnin tarayya Abuja. A kwanakin bayane sojojin kasar Guinea Bissau suka yi juyin mulki hakanan sojojin kasar Benin Republic suma sun yi yunkurin Jhuyin mulkin duk da bai sau nasara ba
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikewa majalisa Bukatar su amince masa ya aika da Sojoji kasar Benin Republic

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikewa majalisa Bukatar su amince masa ya aika da Sojoji kasar Benin Republic

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikewa da majalisar Dattijai da bukatar su amince masa ya aika da sojoji kasar Benin Republic. Kakakin Majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya karanta wasikar da shugaba Tinubun ya aikawa majalisar. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da shugaba Tinubu ya aike da sojoji kasar ta Benin Republic suka hana juyin Mulki da sojojin kasar suka so yi.
Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Duk Labarai
Wani mutum dan kasar Ghana yace wai an masa wahayi cewa nan da ranar Kirsimeti, 25 ga watan Disamba, Duniya zata tashi. Yace wai an Umarceshi da ya kera jirgin ruwa irin na Annabi Nuhu(AS). Yace yan kan kera Jiragen guda 8 manyamanya wadanda kowanensu zasu dauki mutane akalla Miliyan 600. Ya nemi duk wanda suka yadda dashi su zo su tayashi aiki. A cewarsa wai za'a yi ruwa irin na Dufana. https://www.tiktok.com/@ebonoah/video/7554531904482069771?_t=ZS-924jLzUhgZt&_r=1
Da Duminsa: Hukumar Sojojin Saman Najeriya ta fitar da sanarwa kan jirgin saman C-130 dake Burkina Faso da sojoji 11

Da Duminsa: Hukumar Sojojin Saman Najeriya ta fitar da sanarwa kan jirgin saman C-130 dake Burkina Faso da sojoji 11

Duk Labarai
Hukumar sojojin saman Najeriya ta fitar da sanarwa game da jirgin saman C-130 da sojoji 11 dake kasar Burkina Faso. Me magana da yawun hukumar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ne ya fitar da sanarwar inda yace jirgin na kan hanya ne ya samu rangarda inda yayi saukar gaggawa a kasar ta Burkina Faso. Yace wannan shine abinda dokar kasa da kasa ta tanada. Yace jirgin bai taka kowace doka ba kuma suna nan kan bakansu na yiwa dokokin kasa da kasa biyayya. Yace sojojin Najeriyar sun samu tarba me kyau a hannun hukumomin kasar Burkina Faso kuma da zaran komai ya daidaita, zasu ci gaba da tafiyarsu.
Sabbin Rahotanni sun ce Jirgin Najeriya C-130 dake kasar Burkina Faso ya samu Tangarda ne ya sauka a kasar

Sabbin Rahotanni sun ce Jirgin Najeriya C-130 dake kasar Burkina Faso ya samu Tangarda ne ya sauka a kasar

Duk Labarai
Wasu Rahotanni daga bangaren masu goyon bayan Najeriya sun bayyana cewa jirgin saman C-130 da ke kasar Burkina Faso ba tursasa masa aka yi ya sauka ba. Jirgin ya sauka ne saboda samun Tangarda a yayin da yake kan hanya. Saidai hakan na zuwane bayan da ita kasar Burkina Faso tace jirgin ya shigar mata kasa ne ba bisa ka'ida ba. Zuwa yanzu dau hukumar sojojin saman Najeriya basu fitar da sanarwa ba game da lamarin.
Da Duminsa: Kasar Jamhuriyar Nijar tace daga yanzu duk wasu kaya da za’a shigar musu dasu daga Najeriya sai an musu daidai a ga komenene a iyaka kamin a barsu su wuce

Da Duminsa: Kasar Jamhuriyar Nijar tace daga yanzu duk wasu kaya da za’a shigar musu dasu daga Najeriya sai an musu daidai a ga komenene a iyaka kamin a barsu su wuce

Duk Labarai
Kasar Nijar ta fitar da sabuwar doka wadda tace daga yanzu duk wani abu da za'a shigar mata dashi dana Najeriya sai an masa daidai an ga komenene a ciki kamin a barshi ya wuce. Nijar din ta fitar da wannan sabuwar sanarwar ne bayan da Najeriya ta dakile yunkurin juyin mulkin a kasar Benin Republic. Hakanan sanarwar na zuwane bayan da kasar Burkina Faso ta rike jirgin saman Najeriya da sojoji 11 da suka shigar mata sararin samaniyar ta ba bisa ka'ida ba.