Friday, February 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Yanzu haka matarka na can tana cin amanarka da me gidan da kake haya>>Fasto ya gayawa magidanci

Kalli Bidiyon: Yanzu haka matarka na can tana cin amanarka da me gidan da kake haya>>Fasto ya gayawa magidanci

Duk Labarai
Wani fasto ya bayyanawa wani magidanci da ya je cocinsa cewa a yanzi haka matarsa na can tana cin amanarsa da me gidan hayar da yake ciki. Magidancin dai ya gigice zai fita cocin da gudu amma faston yasa aka kamoshi. Ya cewa, faston ya barshi ya je gida, amma faston yace a'a inda yace ba ya son yaje yayi aika-aika, 'yansanda su zo su kamashi suce shine ya tunzurashi. https://twitter.com/i/status/2019376687528792150
Ina son a sayar min da Najeriya dan in gyarata>>Inji Wannan baturen

Ina son a sayar min da Najeriya dan in gyarata>>Inji Wannan baturen

Duk Labarai
Wannan baturen dan kasar Ingila ya nemi a bashi mukamin Firayiministan kasar sannan ya nemi a sayar masa da Najeriya dan ya gyarata. Yace yana son a sayar masa da Najeriya kamar yanda a baya kasarsu ta Ingila ta taba sayen Najeriyar a shekarar 1900. Wannan magana tasa ta jawo cece-kuce inda wasu suka ce sun yadda wasu kuma suka ce ba zai yiyu ba. https://twitter.com/i/status/2019437492588716070
Da Duminsa: Ji Wata magana da Kwankwaso yayi da zata jawo a kamashi a Bincikeshi

Da Duminsa: Ji Wata magana da Kwankwaso yayi da zata jawo a kamashi a Bincikeshi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA sun ce zasu aikawa da hukumar 'yansandan Najeriya da sauran jami'an tsaro korafi dan a biciki tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso kan wani ikirari da yayi. Kungiyar ta bayyana hakane bayan zaman kwamitin zartarwasta, watau NEC Sakataren kungiyar ta NBA, Etaba Agbor ne ya bayyana hakan a shafinsa na X. Maganar da ake zargin Kwankwaso da yi shine, yace a shakerar 2019 ya dauki Abba Kabir Yusuf zuwa ganin alkalan kotun koli ta Najeriya bayan da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta bayyana zaben Kano a matsayin Inconclusive, watau wanda bai kammalu ba. A karshe dai kotun kolin ta tabbatarwa da Gwanduje a wancan lokacin cewa shine yaci zaben. Wannan magana ta tayar da hankuka musamman tsakanin Lauyoyin Najeri...
Da Duminsa: INEC tawa jam’iyyun siyasa biyu Rijista

Da Duminsa: INEC tawa jam’iyyun siyasa biyu Rijista

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, hukumar zabe me zaman kanta, INEC tawa jam'iyyun siyasa biyu Rijista. Shugaban INEC din, Joash Amupitan ne ya bayyana haka a wajan wani taro na musamman a Abuja. Yace jam'iyyun da akawa Rijistar sune, Democratic Leadership Alliance (DLA) da the Nigeria Democratic Congress (NDC). Yace wasiku 171 ne aka gabatar na neman yiwa sabbin jam'iyyu rijista amma guda 2 ne kadai daga cimi suka tsallake.