Thursday, April 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayyana cewa bata yadda da karamin ministan tsaro na Najeriya ba, Bello Matawalle. 'Yar majalisar jihar Florida, Kimberly Daniels ce ta bayyana hakan inda tace suna kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ko dai ya cire Bello Matawalle ko kuma ya canja masa ma'aikata. Hakan na zuwane yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da ta'azzara a musamman Arewacin Najeriya. A baya dai akwai zarge-zargen da ake tawa karamin Ministan tsaron wanda ya sha musantawa
Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Nafiu Bala Gombe da ya fito yace shine shugaban jam'iyyar ADC na riko ya kawo tarnaki a jam'iyyar ya samu matsala da masu daukar nauyinsa. Rahoton yace dama rabin kudin aiki aka bashi idan ya kammala za'a bashi sauran amma yanzu ya nemi a bashi sauran amma sun kiya Saboda sun ce ya kasa hana a yi babban taron jam'iyyar na ADC. Hakanan dakin Otal Din da suke biya masa a Transcorp Hilton sun daina biya Rahoton yace sun babe sosai.
Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Duk Labarai
A wata hira da aka yi da tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, an tambayeshi shin zai iya janyewa Peter Obi takara idan ya lura Peter Obin yafi shi jama'a? Atiku yace zai iya mana. Yace ita takarar siyasa ana samuntane ta hanyar zaben fidda gwani ko kuma ta hanyar samar da dan takara na bai daya. Yace a kowane mataki idan Peter Obi ya zamana shine yayi nasara zai goyi bayansa. https://twitter.com/i/status/2044467777180672111
Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, ta bayyana cewa, Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka sosai fiye dana kasashe masu arziki irin su Amurka, Ingila, da Jamus. Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na X inda yake martani kan bayanan habakar tattalin arziki da kungiyar bayar da lamuni ta Duniya, IMF ta fitar. IMF tace Najeriya zata samu habakar tattalin arziki da maki 4.1 a shekarar 2026. Wannan maki yafi na kasar Amurka wanda IMF tace 2.3 ne sannan yafi na kasar Ingila wanda IMF tace 0.8 ne hakanan yafi na kasar Jamus wanda shima 0.8 ne. Daniel yace Gwamnatin Tinubu ba da wasa take ba.
Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Duk Labarai
Kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF ta bayyana cewa, matsalar tsaron da ake fama da ita ta kai matsayin yaki. Kungiyar tace tana kira ga Gwamnati data karkatar ta hankalinta da ma dukkan wani abu daya shafi kudi dan ganin an magance wannan matsala. Kungiyar ta bayyana matsayar tane bayan zaman data yi. Zaman ya samu halartar Tsohon shugaban sojoji, Janar Tukur Yusuf, Da Tsohon shugaban 'yansanda, Muhammad Abubakar, da tsohon sakataren majalisar Dinkin Duniya, Tijjani Muhammad-Bande, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mahmud Ahmad, da shugaban kungiyar, Bashir Dalhatu. Sun bayyana cewa matsalar tsaron na jefa musamman yankin Arewa cikin tawayar tattalin arziki da kuma daidaita iyalai da sauransu.
Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Duk Labarai
jam'iyyar ADC ta fitar da cikaken bayanin mutanen daga kora daga jam'iyyar inda ta bayyana cewa maciya amana ne kuma sunawa jam'iyyar zagon kasa. Jam'iyyar tace ta dauki wannan mataki ne a babban taronta na kasa data gudanar a Abuja, kamar yanda me magana da yawun jam'iyyar, Bolaji Abdullahi ya sanar. Wadanda aka kora din sune kamar haka, Hon. Leke Abejide, Nafiu Bala Gombe, Mr. Kingsley Temitope Ogga, Mr. Don Norman Obinna, Mr. Kennedy Odion, Mr. Clement Ehigiator, Mrs. Stella Chukwuma, Patrick Ambut, Johny Tovie Derek, Duke Dick, and Elias Adikwu.
Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon Gwamnan kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC duk da cewa kotu ta bayar da belinsa. Mai shari'a na babbar kotun tarayya dake Kaduna, Justice Rilwanu Aikawa ne ya bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai a ranar Talata. Bayan bayar da belin nasa, El-Rufai yaki yin magana da manema labarai amma wani na kusa dashi ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa, kotu ta saka sharuda 10 akan belin na Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Yace sai an cika wadannan sharudanne sannan za'a sakeshi.
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Laraba 15 ga watan Afrilu ya fara ne akan Naira N1,352.25 kowace dala. Farashin ya dan tashi zuwa Naira N1,352.50 kamin daga baya ya koma ya daidaitu a farashin sama. A kasuwar bayan fage kuwa ta Kano, Abuja, da Lagos, Farashin dalar yana akan Naira N1,460 ne zuwa Naira N1,485 akan kowace dala.
Shugaban Amurka, Donald Trump na shirin daukar mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya

Shugaban Amurka, Donald Trump na shirin daukar mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya

Duk Labarai
Wasu majiyoyi daga kafar The Blaze sun bayyana cewa, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump na shirij daukar wani sabon mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya. Rahoton yace, shugaba Trump na shirin daukar matakinne a asirce ba kamar a baya ba yanda ya rika yayatawa ba. Rahoton yace shugaban Amurka, Donald Trump ya fahimci cewa Najeriya na da muhimmanci sosai a nahiyar Afrika kuma duk wanda ya mallaketa ko ya iya juya akalarta, Kamar yana juya akalar gaba dayan Nahiyar Afrika ne. Dan hakane hankalinsa ya koma kan Najeriya. Najeriya tana daga cikin manyan kasashe 5 na kungiyar kasashen dake fitar da danyen man fetur, watau, OPEC, sannan tana da ma'adanan kasa da suka haura dala Tiriliyan wanda ba'a ma fara fito dasu ba.
Kalli Bidiyon yanda mutanen jihar Kwara suka ki karbar Tallafin shugaba Tinubu, Sun ce ba shine matsalarsu ba

Kalli Bidiyon yanda mutanen jihar Kwara suka ki karbar Tallafin shugaba Tinubu, Sun ce ba shine matsalarsu ba

Duk Labarai
Mutanen jihar Kwara sun ki karbar tallafin da aka kai musu na gwamnatin tarayya, karkashin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. A wani Bidiyo da ya rika yawo a kafafen sada zumunta, an ga mutanen na jihar Kwara na cewa basa son tallafin kowa yaki karba. Jihar Kwara dai na daga cikin jihohin dake fama da matsalar tsaro sosai. A baya ma, Jihar Benue sun fito sun ce basa son tallafin shinkafa na Gwamnatin Tinubu inda suka ce ba shine matsalarsu ba. https://twitter.com/i/status/2043695469109313876