Friday, June 26
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta gwamnati a yau, Juma'a, 19 ga watan Yuni, ya kamane akan Naira ₦1,360/$ akan kowace dala. Farashin ya dan yi rawa a tsakanin Naira ₦1,357 zuwa Naira ₦1,364. Farashin a kasuwar bayan fage kuwa yana tsakanin Naira ₦1,390 zuwa Naira ₦1,400, ya danganta mutum idan saye ko sayarwa zai yi.
Cire Naira Biliyan 500 da gwamnatin tarayya ta yi daga Asusun Hadakar Gwamnatoci ya dauki hankula

Cire Naira Biliyan 500 da gwamnatin tarayya ta yi daga Asusun Hadakar Gwamnatoci ya dauki hankula

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta cire naira Biliyan 500 daga asusun hadakar Gwamnatoci kamin a raba kudaden shigar da aka tare tsakanin Gwamnatocin Tarayya, Jihohi da Kananan Hukumomi. Wata Majiya ta tabbatarwa da Jaridar Punchng cewa lallai an cire kudin wanda aka ware dan ko ta kwana musamman a bangaren tsaro. Jaridar tace akawun jihohi wanda dasu ake aikin raba wadannan kudade basu yi korafi akan cire wadannan kudade ba wanda hakan ke nuna cewa suna sane da hakan. A baya ma dai an cire jimullar Naira Biliyan N952bn inda aka baiwa Sojoji, da wasu ma'aikatun Gwamnati da yin ayyukan ci gaba a wasu jihohi.
Ku Daina Watsa labaran mutanen Daji: Gwamnatin tarayya ta gargadi gidajen Jaridu

Ku Daina Watsa labaran mutanen Daji: Gwamnatin tarayya ta gargadi gidajen Jaridu

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta gargadi gidajen Jaridu da cewa, su daina yada labaran tsageran daji. Hakan ya fito ne daga bakin ministan yada labarai Muhammad Idris a wajan wani taro da aka shirya da hadin gwiwar hukumar DSS da kafafen watsa labarai. Yace abin yana bashi takaici yaga shafukan farko na jaridun Najeriya na magana akan harkokin mutanen Daji yayin da ba'a son watsa nasarorin sojoji. Yace wannan abu na watsa labarin abinda tsageran daji suke yi su dama abinda suke son a yi kenan gashi kuma ana musu shi kyauta. Yace ya kama masu kawo rahoto da masu tacewa su san labarin da ya kamata a yada da wanda bai kamata a yada ba dan tsaro da ci gaban kasa.
Bidiyon Update din shugaban daliban jami’ar Gwamnatin tarayya ta FUOYE ya bayyana shi da Budurwarsa

Bidiyon Update din shugaban daliban jami’ar Gwamnatin tarayya ta FUOYE ya bayyana shi da Budurwarsa

Duk Labarai
Bidiyon update din shugaban kungiyar dalibai SUG ta jami'ar FUOYE dake jihar Ekiti me suna James Iyanuoluwa Adio ya bayyana. A Bidiyon an ganshi tare da wata Budurwa inda tuni Bidiyon ya karade kafafen sada zumunta. Hakan na zuwane kwana daya bayan da hukumar makarantar ta dakatar dashi da wasu malamai bisa zargin hada baki su karbi kudin da basa bisa ka'ida daga hannun dalibai. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke masa jaje wasu kuma na masa Ba'a da dariya. Bidiyon yayi muni sosai shiyasa ba zamu iya kawo muku shi anan ba.
Da Duminsa: Hadiza Gabon ta yi sabon post da ya dauki hankula sosai bayan da matar Saleem Goje ta zarge ta da cewa suna soyayya da mijinta

Da Duminsa: Hadiza Gabon ta yi sabon post da ya dauki hankula sosai bayan da matar Saleem Goje ta zarge ta da cewa suna soyayya da mijinta

Duk Labarai
A jiya ne dai Hadiza Gabon ta yi post na farko tun bayan da matar Saleem Goje ta zarge ta da yin soyayya da mijinta. Saidai post din na jiya, Hirace wadda ta yi da wata tauraruwa. A yau kuma Hadiza Gabon ta sake yin wani post inda ta wallafa hotonta na Bidiyon wanda ya dauki hankulan masoyanta da yawa suna ta mata fatan Alheri.