Tuesday, February 17
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bidiyo:G-Fresh Al-Amin Ya bayyana cewa cin amanarsa aka yi aka turo ‘yan Hisbah gidansa

Bidiyo:G-Fresh Al-Amin Ya bayyana cewa cin amanarsa aka yi aka turo ‘yan Hisbah gidansa

G-Fresh Al'amin
Tauraron Tiktok kuma mawaki, G-Fresh Al'amin ya bayyana cewa me masa bidiyo ne ya tura 'yan Hisbah Gidansa. G-Fresh dai ya bayyana hakane a shafinsa cikin wani bidiyo daya wallafa a Tiktok. https://www.tiktok.com/@kanostatematerial/video/7379597342133013765?_t=8n8jNIgp63i&_r=1 Ya bayyana cewa, me masa Bidiyo ne ya ci amanarsa kuma ya kammala bincikensa babu wanda zai gaya masa akasin haka. A baya dai, Hisbah ta kama G-Fresh Al'amin inda aka yi masa nasiha tare da sakashi a Islamiya.

Yadda ake gwajin ciki da allura

Gwajin Ciki
A likitanci da Ilimi na kiwon Lafiya babu wani bayani kan yanda ake gwajin ciki da allura. Saidai akwai wani abu dake faruwa da jariri yayin da wasu mata suka kai sati 16 zuwa 20 da daukar ciki. Wani ruwa na taruwa a mahaifa inda jaririn zai rika shanshi kuma yana kashinshi. Ana kiran abin da sunan Amaniocentesis. Saidai ba duka mata masu ciki ne ke fuskantar wannan matsala ba. To idan abin ya faru, likita kan yi amfani da Allura a tsotse ruwan saboda kada ya rika cutar da uwar da jaririn. Wannan shine kadai muka sani a likitance da ake amfani dashi akan mace me ciki, amma kamar yanda muka fada a farko, a likitanci babu maganar gwajin ciki da Allura.
Akwai yiyuwar Shugaba Tinubu zai yiwa majalisar Zartarwarsa garambawul inda za’a yiwa wasu ministoci canji, za’a kara kirkiro da wasu

Akwai yiyuwar Shugaba Tinubu zai yiwa majalisar Zartarwarsa garambawul inda za’a yiwa wasu ministoci canji, za’a kara kirkiro da wasu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kammala shiri tsaf dan yiwa majalisar zartarwarsa garambawul inda za'a kirkiro karin wasu ministoci da ma'aikatu. Daily Trust tace daga cikin sabbin ma'aikatun da ake son kirkirowa akwai ta kula da dabbobi wadda za'a cire daga ma'aikatar noma. Wannan ma'aikatar ana tunanin zata kawo mafita ga rikicin manoma da makiyaya dake faruwa duk shekara. Hakanan bayan kirkirar sabbin ma'aikatu ana kuma tunanin shugaban kasan zai samar da kananan ministoci a sauran ma'aikatun da basu dasu. Masu kula da al'amuran yau da kullun da masu sharhi a harkokin siyasa sun caccaki gwamnatin Tinubu saboda kin saka kananan ministoci a wasu ma'aikatu
Ba A Bi Umarnin Da Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Bayar Na Sake Fasalin Naira Ba>>Tsohon Daraktan CBN Ga Kotu

Ba A Bi Umarnin Da Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Bayar Na Sake Fasalin Naira Ba>>Tsohon Daraktan CBN Ga Kotu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Tsohon Daraktan Ayyuka na Kudi a Babban Bankin Najeriya (CBN), Ahmed Bello Umar, ya shaida wa babbar kotun Abuja da ke Maitama cewa ba a bi umarnin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar na sake fasalin Naira ba. Ya bayyana cewa takardar kudin Naira da aka sake gyarawa a karkashin tsohon Gwamna Godwin Emefiele sun sha bamban da bayanan da tsohon shugaban kasar ya amince da su. Daga: Abbas Yakubu Yaura
Da Dumi-Dumi: ‘Nan Ba da Jimawa Ba Za Mu Aikawa Majalisa Da Kudirin Doka Kan Sabon Albashin Ma’aikata’ – Tinubu

Da Dumi-Dumi: ‘Nan Ba da Jimawa Ba Za Mu Aikawa Majalisa Da Kudirin Doka Kan Sabon Albashin Ma’aikata’ – Tinubu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce nan ba da dadewa ba zai aika da sabuwar dokar mafi karancin albashi ga majalisar dokokin kasar Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabinsa na ranar dimokradiyya a ranar Laraba. Ya ce gwamnatinsa ba ta murkushe kungiyar kwadago ba kamar yadda gwamnatin kama-karya ta yi. “Mun yi shawarwari cikin nasara kuma mun yi tattaunawa tare da kungiyoyin kwadago a kan mafi karancin albashi na kasa, nan ba da jimawa ba za mu aika da kudirin zartarwa ga Majalisar Dokoki ta kasa domin tabbatar da abin da aka amince da shi a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka,” in ji shi. Ku tuna cewa kwamitin mafi karancin albashi na kasa ya mika rahotonsa ga shugaban kasa a ranar Litinin. A cikin rahoton, gwamnatin tarayya ta gabatar da shawarar mafi karancin alb...
Akwai barazanar ambaliya a jihohi 31 da ƙananan hukumomi 148′

Akwai barazanar ambaliya a jihohi 31 da ƙananan hukumomi 148′

Siyasa
Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA ta ce akwai hasashen jihohin ƙasar 31 da ƙananan hukumomi 148 ka iya fuskantar ambaliya a damunar bana. Hukumar ta buƙaci gwamnatocin jihohin ƙasar da su bi gargaɗinta sannan su aiwatar da matakan kariya daga bala'in ambaliya domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyi al'umma. Shugabar hukumar, Zubaida Umar wadda ta tabbatar da hakan a yayin wata ganawa da jami'an gwamnatin jihar Edo, ta nanata muhimmancin haɗa ƙarfi da ƙarfe da jihar wajen samar da shirin ko-ta-kwana domin tunkarar barazanar ta ambaliya. Hukumar ta NEMA dai ba ta lissafa jerin sunayen jihohin da ƙananan hukumomi ba amma ta ce yawanci birane da garuruwan da ke kusa da ruwa ka iya fuskantar barazanar.
Tinubu bai faɗi nawa albashi mafi ƙanƙanta zai kasance ba a jawabinsa

Tinubu bai faɗi nawa albashi mafi ƙanƙanta zai kasance ba a jawabinsa

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta aike da ƙudiri ga Majalisar Dokokin ƙasar wanda zai kunshi adadin abin da aka amince da shi ya zama albashi mafi ƙanƙanta ga ma'aikata a "matsayin wani ɓangare na "dokokinmu" a shekaru biyar ko ƙasa da haka masu zuwa. Shugaban wanda ya faɗi hakan ne a yayin jawabinsa ga ƴan Najeriya albarkacin ranar dimukraɗiyya, ya ce lallai yana sane da halin matsin tattalin arzikin da 'yan najeriyar ke ciki. To sai dai ya nemi "yan ƙasar da su tallafa wajen cimma "dimukraɗiyyar da za ta tabbatar da cigaban tattalin arziki." Ƴan Najeriya dai sun yi fatan jin ƙarin albashin da suka samu daga bakin shugaban nasu a jawabin nasa na safiyar Talata. A ranar Litinin ne dai kwamitin mutum 37 da aka kafa kan albashin mafi ƙanƙanta ya miƙa rahotonsa bayan kwashe kima...
Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba

Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba

Kwallon Kafa
Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba. Bayan hukuncin INEOS na cigaba da ajiye ten Hag a matsayin mai horas da United, Yanzu shirin ƙungiyar shine ayi gaggawar fara tattauna sabuwar yarjejeniyar tsawaita zaman sa. Manchester United na son nuna amincewar ta gaba ɗaya akan mai horaswar hakanne yasa zata bashi damar ƙara tsawaita zama a Old Trafford domin a cigaba tafiyar tare. Tattaunawa tayi nisa, kaɗan ya rage komai ya kammala! Fagen Wasanni