
Rahotanni daga jihar Borno na cewa sojojin Najeriya 8 ne suka rigamu gidan gaskiya a fafatawar da suka yi da makiya a fagen daga.
Bidiyon gawarwakin sojojin sun bayyana a kafafen sada zumunta inda ake ta alhini.
Amma saboda Munin Bidiyon ba zamu iya kawo muku shi anan ba.
Lamarin dai ya jawo mugane suka ci gaba da kiraye-kirayen ya kamata a kawo karshen matsalar tsaron musamman a Arewa.