Sunday, March 1
Shadow

Duk Labarai

Matasa indai kun shirya da gaske kuke, wallahi cikin sauki zaku kwace mulki daga hannun tsofaffinnan da suka hana kasarnan ci gaba>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Matasa indai kun shirya da gaske kuke, wallahi cikin sauki zaku kwace mulki daga hannun tsofaffinnan da suka hana kasarnan ci gaba>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Duk Labarai
Me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya bayyanawa matasa cewa cikin sauki zasu karbe mulki a kasarnan indai suka ce abinda ake musu ya isa haka. Ya bayyana hakane a wajan wani taron marubuta da aka yi, kamar yanda gidan talabijin na Channels TV ya ruwaito. Sarki Sanusi yace Najeriya ta yi fama da rashin shuwagabanni na gari wanda hakan ya hanata samun ci gaban da ya kamata.
Nima bana neman taimakon Inyas ko taimakon Manzon Allah(SAW), Taimakon Allah kawai nake nema>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Nima bana neman taimakon Inyas ko taimakon Manzon Allah(SAW), Taimakon Allah kawai nake nema>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar ya bayyana cewa, baya neman taimakon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko taimakon Inyass. Yace Taimakon Allah kawai yake nema. Malam ya bayyana hakane a wajan wa'azinsa. https://www.tiktok.com/@isah_bello_assalafy_garo/video/7549655866891422997?_t=ZS-8ziWMkt2bce&_r=1 Marigayi, Dr. Idris Dutsen Tanshi ne ya fara yin wadannan kalamai a baya wadanda suka jawo cece-kuce sosai.
Dangote na sayarwa da kasashen waje mai a farashi me sauki fiye da Najeriya>>’Yan kasuwar mai suka koka

Dangote na sayarwa da kasashen waje mai a farashi me sauki fiye da Najeriya>>’Yan kasuwar mai suka koka

Duk Labarai
'Yan kasuwar man fetur sun koka da cewa, Dangote na sayarwa da kasashen waje man fetur a farashi me sauki fiye ye da yanda yake sayarwa a Najeriya. ''Yan kasuwar sun ce 'yan kasar waje na samun ragin kusan Naira 65 akan kowace Lita idan aka kwatanta da farashin man da Dangoten ke sayarwa a Najeriya. Dan hakane ma suka ce wani lokacin basa saye a wajan Dangote sai su je wajan 'yan kasar wajen da ya sayarwa su saya a hannunsu su shigo dashi Najeriya. Shugaban kungiyar 'yan kasuwar DAPPMAN, Olufemi Adewole ne ya bayyana haka ga manema labarai na Punchng. Yace abinda suke nema a wajan Dangote shine ya rika musu sauki dan haka sai su daina shigo da man daga kasashen waje suna saye a hannunshi. Yace Dangote da gangan yake karya farashin mai da zarar ya ga sun kawo mai daga gasa...
Labarin cewa tsohuwar matar Ahmad XM, Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane

Labarin cewa tsohuwar matar Ahmad XM, Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Labarin dake yawo cewa, tsohuwar matar Ahmad XM, Watau Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane. Safiyar da kanta ta fito ta musanta wannan labari inda kuma wasu na kusa da ita suma duk suka karyata wannan labari. Bayan rabuwarta da tsohon mijinta, Ahmad XM, An yada labaran cewa zata sake aure inda zata auri Hambali, kuma da dama sun zata hakan gaskiyane. Saidai daga baya labari ya bayyana cewa, ba gaskiya bane wannan ikirarin.
Kalli Bidiyon: Rahama Sa’idu ta sake bude babban Shago a Abuja

Kalli Bidiyon: Rahama Sa’idu ta sake bude babban Shago a Abuja

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu ta sake bude babban shago Abuja. Rahama Sa'idu ta sanar da bude shagon nata ne a shafinta na sada zumunta inda aka ga 'yan uwa da abokan arziki ciki hadda mahaifinta sun halarci wajan bude shagon. https://www.tiktok.com/@rahamasaidu2/video/7549712291843837202?_t=ZS-8ziLVPQaxtp&_r=1 Tuni dai da yawa sukai ta mata fatan Alheri ana Allah san barka. https://www.tiktok.com/@rahamasaidu2/video/7549594929803152647?_t=ZS-8ziMBgVk9ez&_r=1
Allah Sarki: Yunusa Ahmadu Yusuf kenan wanda aka fi sani da Buhun Barkono da ya rigamu gidan gaskiya bayan ya shiga dakin Ota da wata me suna Ruth a Abuja

Allah Sarki: Yunusa Ahmadu Yusuf kenan wanda aka fi sani da Buhun Barkono da ya rigamu gidan gaskiya bayan ya shiga dakin Ota da wata me suna Ruth a Abuja

Duk Labarai
Yunusa Ahmadu Yusuf kenan wanda aka fi sani da Buhun Barkono wanda ya rasu a dakin Otal bayan ya shiga shi da wata me suna Ruth. Lamarin ya farune a ranar 8 ga watan Satumba inda bayan sun shiga dakin Yunusa Bai cin abinci saidai yayi ta kwankwadar giya, Kamar yanda rahotonni suka tabbatar. Ruth ta samowa Yunusa maganin kara karfin kuzari wanda bayan da ya sha ne ya suma daga nan kuma sai ya rasu. Tuni aka tafi dashi asibiti dan biciken abinda ya kasheshi. https://twitter.com/DejiAdesogan/status/1966940919791301113?t=zNsWv0rCyXZIrmev5QWxSA&s=19 Lamarin ya farune a Karu-Jikwoyi, Abuja.
Shugaba Tinubu ya cire tallafin man fetur ne saboda ci gaban Najeriya ba tare da damuwa ko za’a sake zabensa ba a 2027>>Inji Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila

Shugaba Tinubu ya cire tallafin man fetur ne saboda ci gaban Najeriya ba tare da damuwa ko za’a sake zabensa ba a 2027>>Inji Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila

Duk Labarai
Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya cire tallafin man fetur ne dan ci gaban Najeriya. Yace shugabab ya yi hakane ba tare da damuwa ko za'a sake zabensa a shekarar 2027 ba. Ya bayyana hakane a wajan wani taron tsaffin 'yan majalisar tarayya daga kudancin Najeriya wanda ya faru a jihar Ogun. Yace tabbas cire tallafin ya kawo wahalhalu amma na dan lokacine. Ya luma kawo misalai irin na tallafin karatun dalibai da sauransu wadanda suka taimaka wajan inganta ilimi da saukaka radadin da mutane ke ji.