Tauraruwar Fina-finan Hausa, Fati Washa kenan a wannan sabon Bidiyon data saki wanda ya dauki hankula sosai.
Mabiyanta sun yaba a yayin da wasu kuma suka kushe.
https://www.tiktok.com/@fatimawasha2/video/7547112423782681863?_t=ZS-8zZvi8aGnWz&_r=1
Tsohon karamin ministan man fetur, Ibe Kachikwu ya bayyana cewa, babu yanda bai yi da tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari ba kan a kara kudin man fetur amma yaki.
Yace Buhari ya ki a kara kudin man fetur ne saboda tausayin talakawa da yake dashi.
Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi.
Kachikwu yace amma daga baya Buhari ya amince inda yace a fara maganar cire tallafin man fetur saidai Ministan yace Buharin yace masa idan hakan bai haifar da da me ido ba, zai sallameshi daga aiki.
Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi kenan a wannan Bidiyon inda yake fada bayan ya kai ziyara wajan gudanar da wani aiki da ya bayar amma ba'a kammala ba.
Da yawa sun jinjinawa gwamnan inda suka ce hakan alamace ta yana aiki tukuru yanda ya kamata.
https://www.tiktok.com/@daddyringim1/video/7547868723315543303?_t=ZS-8zZqkSxEekC&_r=1
Lamarin ya jawo muhawara sosai.
Kalaman Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani na cewa El-Rufai ba me gidansa ne a siyasnce ba sun jawo cece-kuce.
Gwamna Uba Sani ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a Channels TV inda yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da Lauya Gani Fawehinmi ne iyayen gidansa a Siyasa.
Saidai hakan yasa wasu komawa baya a tarihi inda suka zakulo wata tsohuwar magana da Gwamnan ya taba yi inda yace El-Rufai me gidansa ne a siyasa.
Kalli Bidiyon anan
https://twitter.com/ruffydfire/status/1965172721199046804?t=JlN4ww37xQrd-gedOWHb0A&s=19
Malamin Addinin Islama, Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami ya bukaci mutane su daina barin mata a gida suna musu girki kawai.
Malam yace mata ma suna da irin fikirar da Allah ya hore musu wadda za'a iya amfani da ita wajan ci gaban Al'umma.
Dan haka yace kada a ajiye mace girki kawai ta sani, a rika basu dama suna sana'a dan samun taro sisi.
https://www.tiktok.com/@professorisaalipantami/video/7546625822036102407?_t=ZS-8zZnkkEU3iT&_r=1
Malam yace akwai inda mata suke yin abinda maza basu iya yi hakanan akwai inda maza ke yin abinda mata basu iya yi.
Wannan matar ta dauki hankula bayan da ta kwanta kasa tana ta burgimar murna biyo bayan takardar samun aikin data karba bayan shekaru 18 da kammala karatu.
Da yawa sun yi ta tayata Murna.
Danna nan dan kallon Bidiyon
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1965088325683016174?t=TQPsErpVsswPRPJf_xTsug&s=19
Wannan wata matashiya ce da ta zargi wani da kama mata Kirji a motar haya da suka shiga tare.
Ta yi masa Bidiyo inda take Nunawa Duniya fuskarsa yayin da suke cacar baki.
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1965176134041292996?t=sw0Zv2jXUVPF0RDsZeuNTA&s=19
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya nuna damuwa kan yadda bashin Najeriya ya ƙaru zuwa Tiriliyan 149.39 a farkon 2025, kwatankwacin dala biliyan 97, wanda ya wuce iyakar kashi 40% da doka ta gindaya, inda ya kai 52% na GDP.
Abbas ya bayyana haka ne a taron shekara-shekara na ƙungiyar WAAPAC a Abuja, yana mai cewa hauhawar bashin na barazana ga dorewar tattalin arziki, tare da gargadin cewa rancen da ke tallafa wa cin hanci da ciyar da bukatu bai kamata a ci gaba da shi ba.
Ya ce dole rance ya kasance domin ayyukan raya kasa kamar hanya, lafiya, ilimi da masana’antu.
Abbas ya kuma bayyana shirye-shiryen Najeriya na jagorantar kafa tsarin sa ido kan bashin majalisun dokoki a Yammacin Afirka domin tabbatar da gaskiya da tsari.
Kakakin ya jaddada cewa Majalisa za ta tabba...
Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa, akwai yiyuwar Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta koma neman bashi a wajan Opay.
Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shan suka saboda yawan cin bashi.
Kwanannan ADC ta soki shugaban kasar da cewa, bashin da ake bin Najeriya zai iya kaiwa Naira Tiriliyan 200 nan da watan Disamba.
Sakataren yada labarai na ADC, Mallam Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa bashin da shugaba Tinubu ya ciyo yafi wanda shugaba Buhari yaci.
A hirar da aka yi dashi a Arise TV, Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa, Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta jefa dubban 'yan Najeriya cikin yunwa duk da yawan bashin da take ciyowa.
Malaye yace be san dalilin da yasa shugaban ke ciwo bashin makudan kudade ba sannan bai san me yasa 'yan majalisa ke ami...
Hukumar kula da majalisar tarayya ta ki amincewa da komawar sanata Natasha Akpoti majalisar bayan data kammala dakatarwar watanni 6 da aka mata.
Hukumar tace har yanzu dakatarwar da akawa Sanata Natasha na aiki har sai bayan samun hukuncin kotun daukaka kara.
A baya dai sanata Natasha Akpoti ta kai majalisar kotun tarayya amma majalisar ta yi nasara akanta wanda daga baya ta daukaka kara.
Har yanzu dai maganar na gaban kotun daukaka kara wanda majalisar tace ba zata iya daukar wani mataki akan lamarin ba sai bayan hukuncin kotu.