Sunday, March 1
Shadow

Duk Labarai

Kuma Dai: Bayan X, Hukumar DSS ta kuma aikawa Facebook bukatar kulle shafin Sowore

Kuma Dai: Bayan X, Hukumar DSS ta kuma aikawa Facebook bukatar kulle shafin Sowore

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya, DSS ta aikawa da kamfanin Meta me mallakar Facebook da bukatar kulle shafin mawallafin jaridar Sahara Reporters kuma me ikirarin kare hakkin bil'adama, Omoyele Sowore. DSS kamar yanda suka aikawa X sun bukaci cewa, Facebook su kulle shafin Sowore saboda sakon da ya wallafa me cewa shugaban kasa me laifine sannan kuma ya yi karya a Brazil inda yace ya magance matsalar rashawa da cin hanci amma a zahiri bai magance din ba. DSS kamar yanda suka gayawa X sun ce wannan sakon ya kawo matsalar tsaro da cin zarafi ga shugaban kasa da sauransu. Saidai Sowore duk da wannan bai nuna alamar nadama ba.
Ji irin Wilakancin da Inyamuray sukawa El-Rufai a Jihar Imo, sun ce yanda bayya sonsu suma basa sonsa

Ji irin Wilakancin da Inyamuray sukawa El-Rufai a Jihar Imo, sun ce yanda bayya sonsu suma basa sonsa

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kai ziyara jihar Imo tare sa Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Watau Peter Obi. Sun je halartar wani taron bita da aka shirya ne a birnin Owerri na jihar ta Imo ranar Asabar. Saidai sun fuskanci zanga-zanga inda iyamurai da yawa suka taru suka ce El-Rufai ba zai shiga dakin taron ba saboda irin abinda yawa Kiristoci a lokacin da yayi gwamnan jihar Kaduna. Sun kuma ce Peter Obi ya ci amanarsu kuma sun daina goyon bayansa tunda ya kawo musu makiyinsu jiharsu. Rahoton yace masu zanga-zangar inyamurai sun rika daga kwalaye masu dauke da rubutun cewa kai ma Peter Obi ka zama makiyin mu kuma mutuncinka ya zube a idonmu saboda kawo mana El-Rufai. Rahoton yace jami'an tsaro s...
Kalli Bidiyon: Wannan shekarar mun yi Maulidi me tsafta, Ba’a ce an rika ganin Shehu a Sama ko a jikin gini ba, ganin cewa kawai muka rika yi yana wucewa ta gaban mu>>Inji Anisee

Kalli Bidiyon: Wannan shekarar mun yi Maulidi me tsafta, Ba’a ce an rika ganin Shehu a Sama ko a jikin gini ba, ganin cewa kawai muka rika yi yana wucewa ta gaban mu>>Inji Anisee

Duk Labarai
Shahararren dan Darika, Alhaji Anisee Ya bayyana cewa a bana sun yi Maulidi me tsafta. Ya bayyana cewa basu rika ganin Shehu a Gajimare ba ko kuma a jikin gine-gineba, Yace a wannan shekarar sun rika ganin Shehu ne a zahiri yana wucewa ta gabansu. https://www.tiktok.com/@alhajianisee1/video/7547230384145173768?_t=ZS-8zYJAL0uyAL&_r=1
Kalli Bidiyon: Yanda Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami ya fashe da kuka saboda takaicin masu son raba kan Hausawa da Fulani

Kalli Bidiyon: Yanda Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami ya fashe da kuka saboda takaicin masu son raba kan Hausawa da Fulani

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Isa Ali Pantami ya nuna damuwa matuka akan masu son kawo rabuwar kai tsakanin Hausawa da Fulani. A wani wa'azinsa, An ga Malam ya fashe da kuka inda yace yanzu har akwai wanda zai kawo mana kabilanci kuma har a yadda dashi? https://www.tiktok.com/@professorisaalipantami/video/7545900646709595410?_t=ZS-8zYC14zKUIz&_r=1
Kalli Bidiyo: Yanda wasu musulmai a kasar Amurka suka fito suna neman a Haramta Shan giya, Cin Nqmqn Alade da Caca

Kalli Bidiyo: Yanda wasu musulmai a kasar Amurka suka fito suna neman a Haramta Shan giya, Cin Nqmqn Alade da Caca

Duk Labarai
Wannan wasu musulmai ne a kasar Amurka da suka fito suke zanga-zanga dan neman a haramta cin naman Alade da shan giya da caca Lamarin ya farune a Texas inda abin ya matukar dauki hankula sosai wasu na cewa suna da 'yancin yin hakan wasu kuma na ganin yin hakan ganganci ne. Kalli Bidiyonsu a kasa: https://twitter.com/RadioGenoa/status/1964713441899565330?t=xzY6NH0Q3Rz5MgL3aZbY4A&s=19
Kalli Bidiyon: Ana ta cece-kuce, ‘Yan Najeriya na mamaki bayan ganin katafaren gidan tsohon Gwamnan Abia, Orji Kalu a kasar Amurka

Kalli Bidiyon: Ana ta cece-kuce, ‘Yan Najeriya na mamaki bayan ganin katafaren gidan tsohon Gwamnan Abia, Orji Kalu a kasar Amurka

Duk Labarai
An ga katafaren gida na Alfarma da tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Kalu ya mallaka a Maryland dake kasar Amurka. Lamarin ya dauki hankula sosai inda akai ta cece-kuce wasu na fadin cewa abin birgewane inda wasu kuma ke cewa ba da kudinsa ya saya ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1964690041445503097?t=QNJuC22yYEtxJ5F_MOYxzQ&s=19
Baiwa jami’an mu kudi, cin hanci laifi ne, ku daina dauke musu hankali daga gudanar da aiki yanda ya kamata>>Hukumar ‘Yansandan Najeriya ta gargadi mutane

Baiwa jami’an mu kudi, cin hanci laifi ne, ku daina dauke musu hankali daga gudanar da aiki yanda ya kamata>>Hukumar ‘Yansandan Najeriya ta gargadi mutane

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta garagadi Mutane da cewa, baiwa 'yansandan Najeriya kudi ko cin hanci a yayin da suke bakin aiki shima laifi ne. Hukumar ta gargadi 'yan Najeriya da su yi hankali su daina daukewa 'yansandan hankali daga aikin da suke. Sanarwar ta fito ne daga bakin hukumar 'yansandan babban birnin tarayya Abuja. https://twitter.com/FCT_PoliceNG/status/1964752773083181153?t=Hw13v97hldjZVynO-RQ3Lg&s=19
Gwamnati ta shiga tsakani a rikicin Dangote da ‘yan kasuwar man fetur da suke zargin Dangoten da yin kaka gida a harkar man fetur

Gwamnati ta shiga tsakani a rikicin Dangote da ‘yan kasuwar man fetur da suke zargin Dangoten da yin kaka gida a harkar man fetur

Duk Labarai
Ministan Kwadago, Muhammadu Dingyadi ya kira Kungiyar ma'aikatan man fetur ta kasa, NUPENG da kuma kamfanin matatar man Dangote dan ya zauna dasu kan rikicin da ya bulla a tsakaninsu. Kungiyar ta NUPENG ta zargi Dangote da yin kaka gida a harkar man fetur da rashin biyan ma'aikata da kyau da rashin baiwa ma'aikata damar shiga kungiyoyin fafutuka na ma'aikata da sauransu. Kungiyar Tuni ta shirya shiga yajin aiki dan nuna rashin amincewa da tsare-tsaren Matatar mam fetur ta Dangote wanda tace ya sabawa ka'idar aiki wanda kuma tuni Kungiyar Kwadago ta NLC ta amince da wannan yajin aiki. Saidai wannan kira da ministan ya musu ana sa ran dai kawo karshen lamarin.
Kalli Bidiyo: Kafurci da Munafurci ne kesa ake cewa ana tsananin matsalar tsàrò a Najeriya>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Kalli Bidiyo: Kafurci da Munafurci ne kesa ake cewa ana tsananin matsalar tsàrò a Najeriya>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Duk Labarai
Babban malamin addinin Islama, Sheikh Sani Yahya Jingir ya bayyana cewa, Kafurci da Munafurci ne ke sa mutane cewa ana tsanin matsalar tsaro a Najeriya. Malam ya bayyana hakane a yayin da yake wa'azi inda yace su dai sun je jihar Kebbi sun dawo Lafiya. Kalli Bidiyon jawabinsa: https://www.tiktok.com/@i_am_saeed01/video/7546550346475179270?_t=ZS-8zXbRcRPa4W&_r=1