Saturday, February 14
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Duk Labarai
Wannan baiwar Allahn ta bayyana cewa ta karbi Addinin Musulunci inda ta nemi a sakata a addu'a. An ganta da litattafan Addinin Musulunci a Bidiyon data saki Kalli Bidiyon anan https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1 https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1
Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Duk Labarai
Wani sabon Bidiyon 'yan kwallon Najeriya, Super Eagles ya bayyana inda aka ji suna tattauna cewa ba'a biyasu hakkokinsu ba. An dauki Bidiyon ne kamin wasansu da Morocco wanda Moroccon ta fitar dasu a wasan Penalty. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda ake dorawa hukumar NFF alhakin hakan. https://twitter.com/i/status/2012467439267717398
Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da IBB, Obasanjo, Yakubu Gowon da sauran tsaffin Shuwagabannin Najeriya

Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da IBB, Obasanjo, Yakubu Gowon da sauran tsaffin Shuwagabannin Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da tsaffin shuwagabannin Najeriya a cikin shekaru 22 da suka gabata. A wannan shakerar kawai, Gwamnatin ta ware Naira Biliyan 2.3 dan kula da tsaffin shuwagabannin Najeriya. Ana dai kula da bukatun Shuwagabannin Najeriya irin su motocin hawa, kiwon Lafiyarsu, masu musu Hidima, da sauransu duk shekara.
Sati 3 kenan tun bayan da shugaba Tinubu ya tafi kasar waje, ‘yan Najeriya sun fara tambayar lafiya kuwa?

Sati 3 kenan tun bayan da shugaba Tinubu ya tafi kasar waje, ‘yan Najeriya sun fara tambayar lafiya kuwa?

Duk Labarai
Tun ranar 28 ga watan Disamba na shekarar 2025 ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bar Najeriya zuwa Turai. Shugaban ya kuma halarci taron kasashen Duniya dake gudana a kasar UAE. Yanzu sati 3 kenan shugaba Tinubu baya Najeriya. 'Yan Najeriya da yawa a kafafen sada zumunta sun fara tambayar shin ina shugaban kasar ya shigane? Wasu na tambayar Allah sa dai Lafiya. Rahotanni sun bayyyana cewa, Kwanakin shugaba Tinubu 961 akan Mulki saidai a cikin wadannan kwanakin ya shafe wanaki 240 a kasashen waje. Watau a duk cikin kwanaki 4 da yayi yana mulki, kwana daya yayi shi ne a kasashen waje. https://twitter.com/i/status/2012445361525166455 https://twitter.com/i/status/2012480257945681962 https://twitter.com/i/status/2012450978323165459