Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

Wata Sabuwa: Bayan Sakin Tambuwal EFCC na shirin kama shugaban ADC, David Mark

Wata Sabuwa: Bayan Sakin Tambuwal EFCC na shirin kama shugaban ADC, David Mark

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, hukumar EFCC na shirin kama shugaban jam'iyyar ADC, David Marka da kuma tsohon gwamnan jihar Imo, Emeka Ihedioha. Jam'iyyar ADC ce ta bayyana hakan ta bakin kakakinta, Bolaji Abdullahi. Jam'iyyar tace me yasa sai 'yan ADC ne kadai ake wa irin wannan bincike kuma me yasa Misali David Marka da ya bar shugabancin majalisar dattijai kusan shekaru 10 da suka gabata, sai yanzu ne za'a fara bincikensa? ADC ta zargi EFCC da kawar da kai akan 'yan jam'iyyar APC bata bincikensu. Hakan na zuwane bayan sakin tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da EFCC din ta yi bayan kamashi.
Matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin man fetur dinta da Naira 30

Matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin man fetur dinta da Naira 30

Duk Labarai
Matatar man fetur din Dangote ta sanar da rage farashin man fetur dinta da Naira 30.. Me kula da harkar sadarwa na matatar, Anthony Chiejina ne ya bayyana hakan inda yace ragin farashin zai fara aiki ne nan take. Yanzu za'a rika sayen man fetur din akan naira 820 maimakon 850 da ake sayarwa a baua. Matatar tace zata ci gaba da samar da wadataccen man a duka fadin Najeriya
Kalli Bidiyo: Ban yadda ba, Kyamarar BBCHausa ta mayar min da matata tsohuwa>>Inji Gfresh Al-amin

Kalli Bidiyo: Ban yadda ba, Kyamarar BBCHausa ta mayar min da matata tsohuwa>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa bai amince da irin daukar da akawa matarshi ba a yayin hirarsu da BBChausa. Gfresh yace kyamarar BBChausa ta mayar da matarsa tsohuwa. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Tiktok. Gfresh yace matarsa matashiya ce kuma kyakkyawa kuma bai taba auren mata ko yin Budurwa data kai ta kyau da kuruciya ba
Yan sanda sun gargaɗi yara lanana masu tuƙa Adaidaita Sahu a Kano

Yan sanda sun gargaɗi yara lanana masu tuƙa Adaidaita Sahu a Kano

Duk Labarai
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta yi gargaɗi game da yadda yara ƙanana ke tuƙa babur mai ƙafa uku da aka fi sani da Adaidaita Sahu a birnin Kano. Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Litinin ta bayyana damuwa kan yadda ƙaruwar yara ƙananan da ke tuƙa babur mai kafa ukun ke jefa rayukan mutanen jihar cikin haɗari. Sanarwar ta ce a cikin watan Agustan nan kaɗai, an samu manyan haɗurra 16 sanadiyyar tuƙin da yaran suke yi, lamarin da yayi sanadin jikkatar mutane da dama da kuma asarar dukiya mai yawa. ‘Yan sandan sun gargaɗi jama’a da su riƙa bin ƙa’idojin tuƙi tare yin biyayya a duk lokacin da fitilar kan hanya ta nuna a tsaya ko a tafi. Rundunar ƴan sandan ta kuma ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kamawa da hukunta duk wanda aka samu da karya dokokin don tabbatar da ...
EFCC ta saki Tambuwal bayan tsare shi na kwana guda

EFCC ta saki Tambuwal bayan tsare shi na kwana guda

Duk Labarai
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya, EFCC ta saki tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal. Wasu makusantan Sanatan ne suka tabbatar wa BBC sakin nasa, kuma yanzu haka yana gidansa na Abuja. A ranar Litinin ne hukumar ta tsare shi a Abuja, bayan amsa gayyata kan zarge-zargen fitar da maƙudan kuɗaɗe da suka kai Naira biliyan 189. Kamun da aka yi masa ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar, musamman tsakanin ƴan hamayya, waɗanda ke zargin hakan na da alaƙa da rawar da yake takawa a tafiyar ƴan jama'iyyar haɗaka ta ADC.
Bello El-Rufai da Sadiq Zololo sun sayi Kungiyar kwallon kafa ta Ranchers Bees

Bello El-Rufai da Sadiq Zololo sun sayi Kungiyar kwallon kafa ta Ranchers Bees

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai daga jihar Kaduna, Bello El-Rufai tare da Dan wasan kungiyar Real Sociedad, Sadiq Zololo sun sayi kungiyar kwallon kafa ta Ranchers Bees. Kungiyar Kwallon kafa ta Ranchers Bees ta kasance a gasar Premier league ta Najeriya tun daga shekarar 1970. Da yake magana game da sayen Kungiyar, Sadiq ya bayyana farin ciki da kokarin da suke na dawo da martabar kungiyar. Sadiq ya bayyana cewa, ya taso tun yana yaro yake son Kungiyar ta Ranchers Bees.
ABIN FARIN CIKI: Jami’ar Musulunci Ta Madina Ta Ayyana Littafin Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo A Kololuwar Mataki

ABIN FARIN CIKI: Jami’ar Musulunci Ta Madina Ta Ayyana Littafin Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo A Kololuwar Mataki

Duk Labarai
Daga Khalid Yusuf Sambo Kamar yadda a ke ganin a hoton da ke kasa, shahararriyar Jami'ar nan ta Musulunci ta Duniya da ke Birnin Madinar Manzon Allah (S.A.W) ta ayyana Littafin: ضوابط الجرح والتعديل عند الحافظ الذهبي Wallafar Prof. Muhd Sani Umar R/lemo (Hafizahullah) a cikin jerangiyar littafan da za ta yi wa daliban da ke gurbin karatun Digiri na uku (Ph.D) Jarrabawa a cikinsa. Shi ne Littafi daya tilo na mutumin yankin kaf Afirka da ya samu wannan tagomaci. Hakika wannan yana sake nuna karbuwar Littafin da ficensa a Duniyar ilimi. Da ma kuma Littafi ne da ba a shaida kamarsa a bangarensa ba. Littafin shi ne kundinsa na samun shaidar kammala matakin Digiri na biyu a Jami'ar Musulunci ta Madina, wanda a lokacin ya rabauta na samun koluluwar mataki da jinjina mafi girma a fanni...
ADC TA RIKICI A KEBBI: Shugabanin Jam’iyar ADC A Jihar Kebbi Sun Dakatar Da Ciyaman Engr. Sufiyanu Bala Da Mataimakinsa Junaidu Muhd Da Kuma Sakataren Jam’iyyar Hauwa’u Muhammad

ADC TA RIKICI A KEBBI: Shugabanin Jam’iyar ADC A Jihar Kebbi Sun Dakatar Da Ciyaman Engr. Sufiyanu Bala Da Mataimakinsa Junaidu Muhd Da Kuma Sakataren Jam’iyyar Hauwa’u Muhammad

Duk Labarai
ADC TA RIKICI A KEBBI: Shugabanin Jam'iyar ADC A Jihar Kebbi Sun Dakatar Da Ciyaman Engr. Sufiyanu Bala Da Mataimakinsa Junaidu Muhd Da Kuma Sakataren Jam'iyyar Hauwa'u Muhammad A sanarwar da suka fitar ga manema labarai, Shugabannin su sha bakwai dukkansu sun aminta da dakatarwa a bisa zaŕge-zargen da suka gabatar.