Wednesday, July 29
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Idan mace ta fita ba da izinin Mijinta ba ko kuma ta ki amincewa dashi a gado, ya halasta ya daina ciyar da ita>>Inji Sheikh Abdulrahman Isa Jega

Kalli Bidiyon: Idan mace ta fita ba da izinin Mijinta ba ko kuma ta ki amincewa dashi a gado, ya halasta ya daina ciyar da ita>>Inji Sheikh Abdulrahman Isa Jega

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Abdulrahman Isa jega ya bayyana cewa, idan mace taki amincewa mijinta ya taketa ko kuma ta fita bada izininsa ba kuma yayi ta fama da ita ta dawo taki. Malam yace ya halasta mijin ya daina ciyar da ita. Malam yace Addini ne yace haka ba ra'yinsa bane. https://www.tiktok.com/@nuraabunasir/video/7548464538455133447?_t=ZS-8zgh7UyhBSq&_r=1 Malam dai ya bayyana hakane a yayin daya amsa wasu tambayoyi da aka aika masa.
Kalli Bidiyon: Allah ya yadda da Lamarin mu, Wallahi daren jiya na yi mafarki da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Malam

Kalli Bidiyon: Allah ya yadda da Lamarin mu, Wallahi daren jiya na yi mafarki da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Malam

Duk Labarai
Wannan malamin ya rantse da cewa yayi mafarki da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) a daren jiya. Kuma yace idan ba gaskiya bane, kada Allah ya bashi abinda yake nema. Malamin yace Allah ya yadda da lamarinsu. https://www.tiktok.com/@oumardanaljannah/video/7548921608878968086?_t=ZS-8zggS4ex8Jk&_r=1 Malam yace a cikin mafarkin nasa hadda Sayyidina Abubakar (RA).
Yanda me dafa babbar tukunyar Shinkafa ta Najeriya, Hilda Baci ta taka cikin tukunyar ta kuma wanke ta da Mofa ya jawo cece kuce

Yanda me dafa babbar tukunyar Shinkafa ta Najeriya, Hilda Baci ta taka cikin tukunyar ta kuma wanke ta da Mofa ya jawo cece kuce

Duk Labarai
Hilda Baci dake dafa Tukunyar Shinkafa mafi girma a Duniya a Legas ta jawo cece-kuce bayan da aka ganta a cikin tukunyar tana takawa kuma tana gogeta da Mofa. Wasu dai sun rika tambayar tsaftar hakan, amma wasu sun rika cewa mofar sabuwa ce, saidai wasu na tambayar kafarta fa? Hakanan a gefe daya kuma an ga yanda aka rika wanke shinkafar kamin a dafata wanda ya jawo cece-kuce sosai. https://twitter.com/OurFavOnlineDoc/status/1966594966362239433?t=zL0q97rMQdyw_tfINY7yVA&s=19 Hilda Baci dai na son shiga cikin kundin tarihin Duniya.
Karya ake cutar Kanjamau bata kama ni ba>>Inji Shahararren malamin addinin Islama, Zakir Naik

Karya ake cutar Kanjamau bata kama ni ba>>Inji Shahararren malamin addinin Islama, Zakir Naik

Duk Labarai
Shahararren malamin Addinin Islama, Sheikh Zakir Naik ya musanta labaran dake yawo cewa wai cutar kanjamau ta kamashi shi da matarsa kuma an kwantar dasu a asibiti. Malamin ta bakin lauyansa tuni ya karyata wannan ikirari inda yace yana cikin koshin lafiya. Da yawa sun yayata a kafafen sada zumunta cewa cutar HIV ta kama malamain amma labarin ba gaskiya bane.
Ba gaskiya bane, Ban sha komai ba, Matukin jirgin saman Air Peace ya karyata binciken da yace ya sha miyagun Qayoyi da Giyya a lokacin da yake tuka mutane 103

Ba gaskiya bane, Ban sha komai ba, Matukin jirgin saman Air Peace ya karyata binciken da yace ya sha miyagun Qayoyi da Giyya a lokacin da yake tuka mutane 103

Duk Labarai
Matukin jirgin saman air peeace ya musanta sakamakon da aka fitar wanda yace ya sha giya da miyagun kwayoyi a lokacin da jirgin saman da yake tukawa me dauke da mutane 103 yayi hadari. Matukin a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV yace shi bai sha komai ba. Yace sun san irin kudade masu yawa da suka kashe a makarantar horas da tukin jirgin sama, babu yadda za'a yi a rana daya su batawa kansu suna. Yace Asibitin da aka kai jininsu aka yi gwajin hukumar jirgin sama bata amince da ingancinsa ba. https://twitter.com/ARISEtv/status/1966654676750811647?t=65NG7VksvJlfKm8zwcr29Q&s=19 Jirgin dai yayi hadari ne ya sauka daga kan titinsa a filin jirgib sama na fatakwal duk da yake dai ba'a samu asarar rayuka ba
Kalli Bidiyo: ‘Yar Najeriya Hilda Baci ta fara girka Tukunyar shinkafa mafi girma a Duniya dan shiga kundin tarihin Duniya

Kalli Bidiyo: ‘Yar Najeriya Hilda Baci ta fara girka Tukunyar shinkafa mafi girma a Duniya dan shiga kundin tarihin Duniya

Duk Labarai
'Yar Najeriya, Hilda Baci ta fara girka tukunyar Shinkafa mafi girma a Duniya dan ta shiga kudin tarihin Duniya. Tana girkinne a Victoria Island Legas inda mutane da 'yan Jarida suka taru dan ganewa idanunsu yanda zata kasance. https://www.tiktok.com/@hildabaci/video/7549073070871301383?_t=ZS-8zfgU56bXtZ&_r=1 https://www.tiktok.com/@hildabaci/video/7548725143418211591?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7548725143418211591&source=h5_m&timestamp=1757698680&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=...
Likitoci sun fara yajin aiki a faɗin Najeriya

Likitoci sun fara yajin aiki a faɗin Najeriya

Duk Labarai
Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwararewa ta sanar da fara yajin aikin gargadi na kwana biyar daga yau, bisa ga matsayar da aka cimma a majalisar zartarwar ƙungiyar. Ƙungiyar ta bukaci dukkan mambobinta a cibiyoyi daban-daban su bi wannan umarni ba tare da kaucewa ba. A cewar kungiyar, matakin yajin aikin ya zama dole ne domin matsa lamba ga gwamnati kan buƙatunsu na inganta walwala da kyautata yanayin aiki, tare da tabbatar da ingantacciyar tsarin kiwon lafiya ga ‘yan Najeriya. Sun ce makasudin yajin ba wai cutar da al’umma ba ne, sai dai domin tabbatar da nagartar harkar lafiya a kasa. Ƙungiyar ta jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin mambobinta a wannan lokaci, inda ta ce nasarar wannan mataki zai dogara ne akan yadda kowa zai tsaya tsayin daka wajen aiwatar da yajin aikin. ...
Kwanannan za’a daina dauke wuta kwata-kwata a Najeriya>>Inji Gwamnatin Tarayya

Kwanannan za’a daina dauke wuta kwata-kwata a Najeriya>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, Kwanannan za'a daina dauke wutar Lantarki kwatakwata a kasar. Hakan ya fito ne daga bakin ministan wuta, Adebayo Adelabu a wata ganawa da manema labarai a Abuja. Ya bayyana cewa, gwamnati na kokari kan hakan kuma tuni suka fara ganin sakamako me kyau. 'Yan Najeriya sun dade suna kukan rashin tsayayyar wutar lantarki.
Matatar Dangote za ta fara rarraba mai kai-tsaye bayan rage farashinsa

Matatar Dangote za ta fara rarraba mai kai-tsaye bayan rage farashinsa

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote ta sanar cewa za ta fara rarraba man kai-tsaye zuwa tashoshi a duk faɗin Najeriya daga ranar Litinin, 15 ga Satumba. Kazalika, kamfanin ya rage farashin man fetur ga masu gidajen mai zuwa N820 kan lita ɗaya, inda gidajen man jihohin Legas da sauran jihohin yammacin Najeriya za su sayar da shi kan N841. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kamfanin na fitar a shafinsa na X. Sai kuma Abuja da Rivers da Delta da Edo da Kwara za su sayar kan N851. Ta ce daga baya shirin zai karaɗe sauran jihohin ƙasar. Kamfanin ya ce an yi wannan tsarin ne domin rage farashin rarraba man da kuma sauƙaƙa farashin a tashoshi, da kuma rage matsin tattalin arziki. Haka nan, ana sa ran tsarin zai amfani ƙananan masana’antu sama da miliyan 42 ta hanyar rage farashin...