Sunday, February 15
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Gwamna Abba ya bayyana wata Magana da Kwankwaso yayi da bai ji dadinta ba

Kalli Bidiyon: Gwamna Abba ya bayyana wata Magana da Kwankwaso yayi da bai ji dadinta ba

Duk Labarai
An ga wani tsohon Bidiyon gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya na fadar wata magana da Kwankwaso yayi wadda bai ji dadinta ba. Bidiyon dai tsohone amma yana ta yawo a kafafen sada zumunta. An ji Abba yana cewa, Kwankwaso yace idan sun nemi shawara zai basu idan basu nema ba zai zuba musu ido. Saidai Abban yace bai ji dadin wannan magana ba dan har sai da ya je ya samu Kwankwaso akan maganar. https://twitter.com/i/status/2008838947787731344
‘Yan Najeriya sun biya Naira Tiriliyan 1.13 a matsayin kudin wutar Lantarki a watanni 6 da suka gabatà

‘Yan Najeriya sun biya Naira Tiriliyan 1.13 a matsayin kudin wutar Lantarki a watanni 6 da suka gabatà

Duk Labarai
Rahotanni daga hukumar kula da wutar Lantarki ta kasa,NERC sun bayyana cewa, 'yan Najeriya sun biya jimullar Naira Tiriliyan 1.13 a matsayin kudin wutar a cikin watanni 6 da suka gabata. Hakan na zuwane duk da kukan rashin wutar da 'yan Najeriyar ke yi. A shekarar data gabata dai Wutar Lantarkin Najeriya ta samu tangarda sosai. Kuma Gwamnatin ta bayyana cewa kudin tallafin wutar da take bayarwa sun haura Tiriliyan 2.
Babu wani Butulci dan Abba ya koma jam’iyyar APC >>Inji Malam Ibrahim Shekarau

Babu wani Butulci dan Abba ya koma jam’iyyar APC >>Inji Malam Ibrahim Shekarau

Duk Labarai
Tsoho gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana cewa dan Abba ya koma jam'iyyar APC bai ga wani abin Butulci ba. Yace watakila Kwankwaso ya manta amma idan shi ya manta, mutane basu manta ba, yace shima Kwankwason ya canja jam'iyyu. Yace tare suka shiga jam'iyyar NNPP da su Kwankwaso amma rashin Adalci wajan rabon mukamai yasa suka fita dsga jam'iyyar. Yace yawanci dan siyasa na canja jam'iyya ne bayan ya ssmu goyon bayan mabiyansa dan haka bai ga abin ace Abba yawa wani Butulci ba.
Kotu ta bayar da Belin Abubakar Malami

Kotu ta bayar da Belin Abubakar Malami

Duk Labarai
Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarkashin jagorancin alƙali Emeka Nwite ta amince da bayar da belin tsohon ministan shari’a Abubakar Malami da iyalinsa kan kuɗi naira miliyan 500 da kuma mutum biyu da za su tsaya musu. A cewar alƙalin, mutanen da za su tsaya musu sai sun kasance suna da filaye a yankunan Asokoro da Maitama ko Gwarinpa, sannan kuma sai sun miƙa dukkan takardun tafiyarsu ga kotu. Kwanakin baya ne dai hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ta gabatar da tuhume-tuhume 16 a kan Malami da iyalinsa masu alaƙala da halasta kuɗaɗen haram da kuma mallakar kadarori da darajarsu ta haura naira biliyan 8.7 wanda ya kai ga tsaresu a gidan yarin Kuje da ke Abuja.