Ɗan Tsohon Shugaban Kasa, Malam Umaru Musa Yar'adua, Musa Umaru Musa Yar'adua Ya Ziyarci Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo A Gonarsa Dake Otta Jihar Ogun.
Daga Jamilu Dabawa
Malamai A Faɗin Nijeriya Sun Fara Kiraye-Kirayen A Taka Wa Malama Juwairiyya Birki Saboda Salon Wa’azinta Yana Gurɓata Tarbiyya.
Biyo bayan wa’azozin da ake zarĝiɲ Malama Juwairiyya take gabatarwa masu cike da labarai masu alaƙa da yâɗa fașãḍi da ɓarna cikin al’umma, wasu malamai a Najeriya sun fara kiraye-kirayen a takawa Malama Juwairiyya birki sabøda wa’azinta yana kama da gurɓâta tarbiyyar ƴaƴa mata da matan aure da ƴân mata, inji Malaman kamar yadda Dokin Karfe TV ta ruwaito suna cewa.
A cewar ɗaya daga cikin matasan Malaman, Dakta Jamilu Aliyu, "Ke fășiƙâ ce, a gaban maza da mata an haɗa su a wajen Walima ki zo kina cewa wai kawai kuna tafiya sai ga wata azzâkãriɲ namiji na roba ya faɗo daga jakarta kika tsaya kina kallonta. Wannan labarin fa kina bayarwa ne Duniya tana kal...
Wani Kwamandan Sojojin Najeriya a Arewa maso gabas inda ake fama da karuwar hare-haren 'yan Bindiga na Bòkò Hàràm ya bayyana cewa ba zasu kyale ba, sai sun dauki fansa.
A kalla sasanin sojoji 10 ne mayakan Bòkò Hàràm da ÌŚWÀP suka farmawa da hare-haren.
Shugaban hedikwatar tsaro ta kasa, Christopher Musa ya bayyanawa sojojin cewa aka kokarin kai musu sabbin makamai kuma za'a magance matsalar ta tsaro inda ya karfafa musu gwiwa yayin ziyarar da ya kaiwa sojojin Borno.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa, shuwagabannin Najeriya da suka zo bayan Obasanjo ne ke da Alhakin dawowar Kungiyar Bòkò Hàràm.
Ya bayyana hakane a Abuja a yayin ziyarar da wasu 'yan siyasa daga jihar Kogi suka kai masa.
Yace kungiyar ta fara bayyanane a shekarar 2002 a jihar Yobe
Yace suna sumun labari, Obasanjo ya aika aka kirashi yace mai ya yake ganin za'a bullowa wannan lamari? Sai yace masa a kira shuwagabannin tsaro a basu lokaci su gama da kungiyar, idan suka kasa sai a sauke su a nada wasu.
Yace haka kuwa aka yi kuma aka murkushe kungiyar.
Yace bayan sun sauka Mulki ne wanda suka hau suka yi sakaci kungiyar ta dawo.
Hukumar NBS dake kula da kididdigar alkaluma a Najeriya ta fitar da bayanan Alkaluma kasuwanci da kayan Masarufi na watan maris.
Hukumar tace alkaluma sun nuna makin farashin kayan masarufi ya tsaya a mataki na kaso 23.71 cikin 100.
Hakan na nufin farashin kaya masarufi sun yo kasa idan aka hada da alkaluma baya da aka samu.
Saidai Jihohin Enugu, Kebbi, Niger, Benue, Ekiti, Nassarawa, Zamfara, Delta, Gombe, Sokoto, da babban birnin tarayya Abuja, nasu Alkaluman sama suka yi.
Rahoton yace wadannan jihohi alkaluansu sun nuna suna da maki 30 cikin 100 na hauhawar farashin kayan masarufi.
Wannan wani dan shekaru 50 ne da aka kama bisa zargin baiwa 'yan Bindiga bayanan sirri a jihar Katsina.
Ya amsa laifinsa.
https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1922753828597764387?t=S7oXlZgDtTseqTaAGozfEw&s=19
Allah ya kyauta.
Dan gidan Gwamnan jihar Anambra, Ya dauki hankula bayan da aka ganshi da baturiya budurwarsa suna shakatawa a kasar Waje.
Bidiyon ya dauki hankula inda akai ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi daban-daban.
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1922988630781390911?t=b7NoSvFKsAxNgW8JJHEdGQ&s=19
Badai a bayyana a wace kasa ce yake ba.
Dan majalisar Wakilai daga jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa ya nemi a baiwa 'yan Najeriya dama su rike makamai dan baiwa Kansu Kariya.
Ya bayyana hakane a farfajiyar majalisar Wakilai inda yace idan jami'an tsaro sun kasa, kamata yayi a baiwa 'yan Najeriya damar kare kansu.
https://twitter.com/General_Somto/status/1922760426145620359?t=W744pEzgJuQRYfcSdcw8pg&s=19
A baya dai Tsohon Ministan matasa da wasanni, Solomon Dalung da Lauya dan fafutuka, Deji Adeyanju, da Janar T.Y Danjuma duk sun nemi a baiwa 'yan Najeriya damar daukar Makamai dan kare kansu