Gwamnatin Kano ta dakatar da watsa shirye shiryen siyasa kai tsaye a kafafen yada labarai dake jihar. Hakan na zuwa ne domin tantance da kuma tsabtace kalamai da yan siyasa ke yi a kafar sadarwa na radiyo da talabijin
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye a Kafafen Watsa Labarai
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana dakatarwa nan take ga dukkan shirye-shiryen siyasa da ake yadawa kai tsaye a kafafen watsa labarai na jihar.
An bayyana wannan mataki ne yayin taron tattaunawa na kowane lokaci da ake gudanarwa a Ma’aikatar Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, wanda Kwamishinan Yada Labarai, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya jagoranta tare da shugabannin kafafen yada labarai.
A cewar wata sanarwa da Daraktan Harkokin Musamman na ma’aikatar, Sani Abba Yola, ya sanyawa hannu, an dauki wannan mataki ne don dakile yada kalaman da za su iya haifar da fitina da barazana ga zaman lafiya da daidaiton al’adu da addini a jihar.
“Ba mu dauki wannan mataki don murkushe ‘yan adawa ba,” in ji ...








