Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya sanar da cewa ya bar jam'iyyar APC a cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Litinin.
El-Rufai ya ce zai yi aiki tuƙuru domin haɗa kan jam'iyyun adawa da sabuwar jam'iyyarsa ta SDP domin ƙalubalantar APC
Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Rivers, Tony Okocha ya baiwa gwamnan jihar, Siminalayi Fubara zabin ko dai ya ajiye mukaminsa salin Alin ko kuma a tsigeshi.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai ranar Litinin a babban birnin na jihar watau Fatakwal.
Ya bayyan gayyatar da Fubara yawa 'yan majalisar jihar da cewa ta mugunta ce.
Okocha yace sun baiwa Gwamna Fubara awanni 48 ya sauka ko a tsigeshi.
Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta kama wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan fashin daji waɗanda ake zargin suna kan hanyarsu ta sayen bindigar AK-47.
Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna, ya tabbatar da cafke waɗanda ake zargin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.
A cewarsa, rundunar ta samu gagarumar nasara a kokarinta na dakile yaduwar ‘yan fashin daji da miyagun laifuka a jihar.
Ya ce, “A ranar 6 ga Maris, 2025, da misalin karfe 2:00 na rana, wata tawagar jami’an bincike na ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin SP Ahmad Abdullahi, jami’in da ke kula da ofishin 'yansanda na Jar Kuka, sun cafke wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan bindiga a gidan man Chula dake Hotoro a Kano.
“Waɗanda aka kama sun haɗa da Shukurana Salihu, mai shekara 25; Rabi’u Dahiru, mai s...
Yayin da har yanzu gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata cika shekaru 2 da kafuwa ba, an fara yakin neman zaben 2027 dan ganin ya zarce.
Duk da yake shi shugaban kasar ko Jam'iyyar APC a hukumance basu bayyana fara yakin neman zaben ba.
Amma wasu jigo a Gwamnatin irin su shugaban Jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Sakataren Gwamnati, George Akume sun bayyana neman Shugaba Tinubu ya zarce.
A yayin da yake ganawa da wasu 'yan Jam'iyyar a hedikwatar Jam'iyyar dake Abuja, Ganduje yace 'yan siyasa masu son tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2027 su dakata sai bayan 2031 idan Tinubu ya gama wa'adinsa na shekaru 8 akan mulki.
Hakanan shima Akume a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV yace yace Atiku Abubakar ya dakata da neman zama shugab...
Rahotanni sun nuna cewa, duk da cewa a yanzu akwai matatun man fetur dake tace mai a gida Najeriya, amma a shekarar 2024, yawan tataccen man fetur din da ake shigo dashi daga kasar waje ya nunka.
Rahoton hukumar kididdiga ta kasa, NBS ya bayyana cewa, kudin da ake kashewa dan shigo da man fetur din ya nunka inda yake a kaso 105.3 cikin 100 kamar yanda rahotanni suka nunar.
Inda a shekarar 2023 an kashe Naira N7.51tn wajan shigo da man fetur din amma a shekarar 2024 Naira N15.42tn ne aka kashe wajan shigo da tataccen man fetur din daga kasashen ketare.
Hakan na zuwane yayin da ake tsammanin cewa za'a samu raguwar dogaro da kasashen waje wajan siyen tataccen man fetur din musamman ma ganin matatar Dangote tana aiki hakanan an tayar da wasu matatun man fetur na Gwamnati.
Rahotanni sun bayyana cewa hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta EFCC ta kwato kudade da yawa wanda bata taba kwato kamarsu ba tunda aka kafata.
Hukumar ce da kanta ta fitar da wannan sanarwa inda tace yawan kudaden data kwato sun kai Naira N364bn.
Sannan tace ta samu nasarar kulle mutane mahandama 4,11 jimullar kudaden da EFCC tace ta kwato sun hada da N364.6 billion, $214.5 million, £54,318.64, €31,265, CAD$2,990, sai kuma AUD$740.
Hukumar tace kuma wasu daga cikin kudaden an yi amfani dasu ne wajan ayyukan gwamnati dake amfanin 'yan Najeriya kamar bayar da bashin karatu ga dalibai.
Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya gargadi 'yan Najeriya da su daina tsoma baki akan abinda basu da ilimi akansa.
Ya jawo hankalin 'yan Najeriya da cewa, su fahimci dokokin majalisar kamin su tsoma baki akan harkokinta.
Ya bayyana hakane a yayin da wasu kungiya daga yankinsa na Niger Delta suka kai masa ziyara.
Hakan na zuwane a yayin da ake ta bayyana ra'ayoyi mabanbanta game da dambarwarsa da Sanata Natasha Akpoti.
Ya bayyana cewa masu sharhi akan al'amuran majalisar ba tare da sanin dokokinsu ba kamar me maganin gargajiyane dake son fassara Baibul ko wanda ba Musulmi ba yayi kokarin fassara Qur'ani.
Akpabio yace kujerar da yake kai rabon yankinsu na Niger Delta da samunta tun shekaru 46 da suka gabata yace kuma ba dan shi bane yake kan kujerar, yana ...
Jihar Kebbi ta gabo karin ma'adanai na karkashin kasa a jihar.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Yakubu Ahmed-BK ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.
Yace an gano karin ma'adanan ne a Jega, Dandi, Gwandu, Suru, Birnin Kebbi, Argungu da sauransu.
Wannan na zuwane a yayin da jihar Kebbi ke da ma'adanai kamar su gwal da sauransu.
Ya bayyana gano wadannan karin ma'adanai da cewa, wata hanyace ta karin samun kudin shiga ga jihar.
Kungiyar Limaman Kiristoci na darikar Katolika sun bayyana cewa matsalar talauci, rashin aikin yi tsakanin matasa da matsalar tsaro na karuwa a Najeriya.
Kungiyar ta bayyana hakane a zaman ta a Abuja ranar Labadi inda ta nemi shugaba Tinubu da ya dauki matakin gyara.
Zaman wanda ya samu halartar shugabannin Kungiyar Most Rev. Lucius Ugorji, Archbishop na cocin Owerri da shugaban CBCN, Archbishop Daniel Okoh, da kuma shugaban Kungiyar Kiristoci ta Najeriya, Christian Association of Nigeria (CAN); da Most Rev. Ignatius Kaigama, Catholic Archbishop of Abuja ya yi na'am da matakan Gwamnati na gyara amma yace matakan sun yi kadan.
Shugaban kwamitin da'a na majalisar dattijai Sanata Neda Imasuen wanda shine ya bayar da shawarar a dakatar da Sanata Natasha Akpoti tsawon watanni 6, shi kuma kasar Amurka ta hanashi shiga kasarta saboda zargin rashawa da cin hanci.
Yana da kamfanin aikin Lauya, kuma wata mata ta kawo masa aikin ya wakilceta a kotu, saidai maimakon ya wakilceta, bayan da ta biyashi kudin aiki, sai ya tsere da kudin ba tare da ya je ya wakilceta a kotun ba.
Hakanan rahoton yace an nemi a bincikeshi amma yaki.
Matar me suna Daphne Shyfield a shekarar 2009 ta baiwa Sanata Neda makudan kudade ya wakilceta a kotu amma ya tsere da kudinta kuma yaki wakiltarta a Kotu.