Monday, May 11
Shadow

Duk Labarai

Ƴansanda sun kama wata mata bisa zargin kàshè kishiyarta a Bauchi, bayan ta kkàsheta, ta kuma watsa mata ruwan zafi sannan ta tattara buhu ta cinnawa gawar wuta

Ƴansanda sun kama wata mata bisa zargin kàshè kishiyarta a Bauchi, bayan ta kkàsheta, ta kuma watsa mata ruwan zafi sannan ta tattara buhu ta cinnawa gawar wuta

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta ce ta kama wata mata mai suna Fatima Mohammed kan zargin kashe kishiyar mai suna Hajara Isa hanyar shaƙeta a gidan mijinsu. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ahmed Wakil ya fitar ranar Talata ya ce tuni rundunarsu ta ƙaddamar da bincike kan lamarin. Ya ce mijin matan - Sale Isa - ne ya kai ƙorafi wajen ƴansanda a ranar Talata. Wakil ya ce bayan fara gudanar da bincike ƴansanda suka kama matar mai suna Fatima Mohammed mai shekara 28, wadda daga baya ta amsa laifinta a lokacin ƴansanda suke tuhumarta. “A lokacin da ake tuhumarta ta amsa laifinta inda tace shaƙe kishiyartata ta yi, har sai da ta mutu'', in ji sanarwar. Sanarwar ta ƙara da cewa ''bayan ta kashe ta, ta yi ƙoƙarin yin ɓadda-bami, ta yadda ba ...
Karya Sanata Natasha take min mamana ta min tarbiyya me kyau, bana cin zarafin mata>>Sanata Godswill Akpabio

Karya Sanata Natasha take min mamana ta min tarbiyya me kyau, bana cin zarafin mata>>Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Sanata Godswill Akpabio kakakin majalisar dattijai ya bayyana cewa, Karya sanata Natasha Akpoti ke masa da tace ya nemi yin lalata da ita. Ya bayyana hakane a zaman majalisar na ranar laraba. Inda yace shi bai taba cin zarafin kowace mace ba a rayuwarsa ya kara da cewa shi har kyautar girmamawa aka bashi saboda kare hakkin mata. Sanata Natasha Akpoti dai ta zargi kakakin majalisar dattijan da neman yin lalata da ita shiyasa baya bata damar gabatar da ayyukan ci gaba a majalisar.
Motar ‘yansanda ta kashe karamar yarinya a wajan bin me laifi

Motar ‘yansanda ta kashe karamar yarinya a wajan bin me laifi

Duk Labarai
Motar 'yansanda a jihar Legas ta kashe wata karamar yarinya me shekaru 6 a yayin da suke bin wani me laifi. Lamarin ya farune a yankin Iyana Ipa dake birnin Legas. Mahaifin yarinyar, Nnamdi Ugorji ya bayyanawa majiyarmu cewa, 'yansanda daga ofishin 'yansandan na Mosholashi ne suka biyo me laifi inda a haka ne suka buge diyarsa me shekaru 6 ta mutu. Yace diyarsa da 'yan uwanta sun je banki ne ciro kudi a kan hanyar ne motar 'yansandan ta bugesu, yace kuma 'yansandan sun so canjawa lamarin fasali inda suke nuna cewa motarsu ta yi kulikulin kuburane. Yayi kira ga shugaban 'yansanda da shugaban kasa da ministar mata da su tabbatar wanda suka aikata wannan lamari an hukuntasu.
Kalli bidiyon yanda Sheikh Pantami ya fashe da kuka saboda shaukin son Annabi(SAW) yayin da yake wa’azi, lamarin ya jawo cece-kuce

Kalli bidiyon yanda Sheikh Pantami ya fashe da kuka saboda shaukin son Annabi(SAW) yayin da yake wa’azi, lamarin ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Babban malamin addinin islama, kuma tsohon ministan sadarwa, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya fashe da kuka yayin da yake bayar da tarihin Yakun Uhud. Saidai lamarin ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta. Wasu sun rikawa malam shaguben cewa da yana kan mulki rike da mukamin minista ya daina kuka inda wasu suka rika cewa yanzu da babu mukamin shine kukan nashi ya dawo. https://www.tiktok.com/@ukashabeenabdullahi/video/7478000163596832055?_t=ZM-8uQathS8...
Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Duk Labarai
Bankin (Afreximbank) ya bayyana cewa, Najeriya ce kasa ta 3 a jerin kasashen da suka fi yawan cin bashi a Africa. A wani bayani da ya fitar, bankin yace yawan ciyo bashi daga kasashen waje a tsakanin kasashen Adrica na ci gaba da karuwa. Yace hakan na faruwane saboda rashin ci gaban bangaren hada-hadar kudi na kasashen Afrikan. Bankin yace a watanni 6 na farkon shekarar 2024, kasashen Afrika 10 ne ke da kaso 69 na yawan bashin da aka ciwo a nahiyar. Kasashen sune South Africa (14%), Egypt (13%), Nigeria (8%), Morocco (6%), Mozambique (6%), Angola (5%), Kenya (4%), Ghana (4%), Côte d’Ivoire (3%), sai Senegal (3%). Bankin yace hakan na kara karuwane saboda yawan dogaron da kasashen ke yi da samun kudi ta hanyar neman tallafi daga kasashen yamma.
Da Duminsa: Kotu ta dakatar da Yunkurin ladaftar da sanata Natasha Akpoti da majalisa ke shirin yi

Da Duminsa: Kotu ta dakatar da Yunkurin ladaftar da sanata Natasha Akpoti da majalisa ke shirin yi

Duk Labarai
Babbar kotun tarayya dake Abuja ta dakatar da yunkurin ladaftar da Sanata Natasha Akpoti da majalisar tarayya ke shirin yi. Lauyoyin Sanata Natasha Akpoti ne suka shigar da kara inda suke neman kotun ta dakatar da kwamitin ladaftarwa dake neman tuhumar sanata Natasha Akpoti. Mai Shari'a Justice Obiora Egwuatu ya amince da wannan bukata inda yace an dakatar da wannan bincike. Yanzi dai majalisar ba zata iya ci gaba da binciken sana Natasha Akpoti ba har sai idan an samu daukaka kara ko wani sabon hukuncin ya fito.
A wannan shekarar kowa zai ga amfanin gyare-gyaren da gwamnatina ta yi, za’a ji dadi>>Gwamnatin Tinubu

A wannan shekarar kowa zai ga amfanin gyare-gyaren da gwamnatina ta yi, za’a ji dadi>>Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, a wannan shekarar da muke ciki ne za'a fara shaida romon gyare-gyaren da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu ta yi. Wasu daga cikin gyare-gyaren da Gwamnatin ta yi sun hada da cire tallafin man fetur, kara kudin wutar lantarki, kara kudin kira dana data, wanda wadannan abubuwa sun jefa 'yan Najeriya cikin matsi. Saidai da yake magana kan lamarin, Ministan yada labarai, Muhammad Idris ya bayyana cewa a wannan shekarar da muke ciki za'a fara ganin amfanin wadannan gyare-gyaren. Ya bayar da misali da kasafin kudin shekarar 2025 na Naira Tiriliyan 54.2 wanda yace tun da ake a kasarnan ba'a taba yin kamarsa ba. Yace wannan kasafin kudi an tsarashine dan kawowa 'yan Najeriya ci gaba da saukin rayuwa.
Babu wanda ya isa ya sauke Sanata Godswill Akpabio daga mukaminsa saboda wannan dan zargin da Natasha tai masa>>Inji Basaraken jihar Bayelsa

Babu wanda ya isa ya sauke Sanata Godswill Akpabio daga mukaminsa saboda wannan dan zargin da Natasha tai masa>>Inji Basaraken jihar Bayelsa

Duk Labarai
Basaraken jihar Bayelsa kuma shugaban sarakunan jihar, Bubaraye Dakolo Agada IV, ya bayyana cewa babu wanda ya isa ya sauke Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio. Ya bayyana cewa saboda wannan dan zargin da sanata Natasha Akpoti ta yi masa, bai isa ya sa a saukeshi ba. Yace su suna tare da Sanata Godswill Akpabio saboda dansu ne. Yace ya kamata awa Sanata Akpabio adalci kuma a kafa kwamitin bincikw da zai binciki lamarin. Yace Sanata Godswill Akpabio ya kawowa Najeriya ci gaba sosai.