Monday, February 16
Shadow

Duk Labarai

‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

Duk Labarai
Masana harkokin lafiya a Najeriya sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta aike da tawagar likitoci na musmaman da suka kware kan cututuka masu yaɗuwa zuwa Borno saboda fargabar barkewar cututuka sakamakon ambaliyar ruwan da aka fuskanta a jihar. Masanan sun ce, suna fargabar barkewar cututuka irinsu zazzabin cizon sauro, da Zika, da zazzabin typoid, da na dange, da kuma uwa uba amai da gudawa, sakamakon irin dattin da ambaliyar ruwa ta kwaso da gawarwakin makabartu da ruwan ya dauko. Dr Nasiru Sani Gwarzo, babban sakataren ma'aikatar Ilimi a Najeriya, kuma masani kan harkokin kiwon lafiya ya shaida wa BBC cewa, dole ne hukumomi su gaggauta shawo kan ruwan da ya malale asibitin koyarwa na Maiduguri saboda wasu daga cikin na'urorin asibitin akwai wadan ke da sinadarin nukiliya a ciki da k...
Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote ta musanta ikirarin kamfanin mai na kasa,NNPCL da yace ya sayo mai na farko daga Dangote akan farashin Naira 898 akan kowace lita. Me magana da yawun kamfanin,Mr Olufemi Soneye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace da dala aka sayar musu da danyen man fetur dun da suka saya dan haka suma da dala suka sayarwa da kamfanin na NNPCL da tataccen man fetur din. Ya bayyana cewa kuma mansu zai isa kowane sako da lungu na kasarnan. Yace a saurari kwamitin da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kafa kan lamarin shine zai bayyana farashin man nasu.
Obasanjo,Abdulsalam, da Ali Gusau da IBB sun yi zama na musamman kan halin da Najeriya ke ciki

Obasanjo,Abdulsalam, da Ali Gusau da IBB sun yi zama na musamman kan halin da Najeriya ke ciki

Duk Labarai
Tsaffin shuwagabannin kasa,Olusegun Obasanjo,Janar Ibrahim Badamasi Babangida, Abdulsalam Abubakar da Janar Ali Gusau sun yi zama na musamman a kan halin da Najeriya ke ciki. Sun yi zamanne a gidan tsohon shugaban kasa, IBB dake Minna. Wata majiya ta bayyana cewa, Rahotannin sun nuna an yi zamanne kan matsalar da Najeriya ke ciki musamman halin matsin tattalin arziki.
A farashin 898 muka sayi man fetur daga matatar man Dangote>>NNPCL

A farashin 898 muka sayi man fetur daga matatar man Dangote>>NNPCL

Duk Labarai
Kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya bayyana cewa, a farashin Naira 898 suka sayi man fetur daga matatar man fetur ta Dangote. A yau ne dai kamfanin na NNPCL suka fara daukar man fetur din daga matatar man ta Dangote bayan shan dambarwa tsakanin Gwamnati da matatar man. Masu sharhi da yawa na ganin cewa, sayen man fetur din a wannan farashin daga matatar Dangote na nufin bata canja zani ba. Inda wasu ke zargin cewa, Gwamnati ce ta yi kaka gida a lamarin shiyasa man yayi tsada haka. A baya dai ana tsammanin matatar man fetur ta Dangote zata kawo saukin Man fetur a kasarnan amma hakan da kamar wuya.
Kalli Bidiyon yanda mataimakin shugaban kasa ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi

Kalli Bidiyon yanda mataimakin shugaban kasa ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu, Paul Mashatile ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi. Bidiyon faruwar lamarin ya yadu a kafafen sada zumunta sosai. Lamarin ya farune a garin Tzaneen dake Limpopo na kasar. https://www.youtube.com/watch?v=ueg3tH9HQPo?si=6TJ8xuSioycqCIlS Rahotanni sunce mataimakin shugaban kasar ya fadi ne saboda tsananin zafi da ake yi. Ba dai a kaishi Asibiti ba dan lamarin bai yi muni ba.
Sojan da ya daure Abbas tsawon shekara 6 saboda ya je Sallah na shan Tofin Allah Tsine

Sojan da ya daure Abbas tsawon shekara 6 saboda ya je Sallah na shan Tofin Allah Tsine

Duk Labarai
Sojan Najeriya, M.S Adamu wanda ake zargin ya daure karamin soja, Abbas na shan Allah wadai da kiran a hukuntashi saboda hukuncin da yawa Abbas yayi tsauri. Matar Abbas ce dai ta je kafar Berekete Family inda ta bayyana cewa an daure mijinta bayan da yaje Sallah ya dawo ba tare da neman izini ba. Sannan ogansa na magana shima yana magana. An daureshi dai bayan da kansa ya daku ya rika fitar da Jini wanda hakan yasa kwakwalwarsa ta tabu ya samu tabin hankali. Daga baya dai an kaishi Asibiti aka masa magani.
Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000

Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000

Duk Labarai
TSANTSAR RASHIƝ IMÁNI DA TAÚSÁYI Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000. Mijinta soja ne Mųsưlmi wanda daga zuwa yin Sálląh yayin da ake bakin aiki shine ogansa ya sa shi a gaba shekara da shekaru a garƙame sai da ya haukatar da shi. Tsantsar tsagwaron rashin imani ya ƙare a wannan labarin. Shin ina manyan Musulmi dake aikin soja a ƙasar nan? Shin wa ya ce a keta alfarmar ɗan adam saboda bambancin addini a aikin soja? Ina kungiyoyin kare hakkin mata? Ina kungiyar kare hakkin dan Adam? Ina kungiyar manyan Arewa? Ina kungiyar lauyoyi Musulmi? Ina kungiyar Malaman mu? Ina kungiyar yan jaridun kasar nan? Mutun ya sadaukar da rayuwar sa don ya kare ƙasa amma a ƙarshe saboda son zuciyar wani a mayar da...
Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar

Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar

Duk Labarai
Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar. Waɗanda suka addabi al'ummar jihar Zamfara da sauran jihohin Arewa. An tabbatar da jarumi ne na yankan shakku, domin ance harda hannu yake kama ƴan bindiga. Allah ya ƙara kare shi a wannan aiki da yake yi. Ya kuma ƙara bashi nasara da sauran abokan aikinsa. Daga Zakari Y Adamu Kontagora