Friday, January 23
Shadow

Duk Labarai

Ba lallai sai kana da Karatun Bo-ko bane sannan zaka yi nasara a rayuwa>>Inji Shugaban kasar Ingila

Ba lallai sai kana da Karatun Bo-ko bane sannan zaka yi nasara a rayuwa>>Inji Shugaban kasar Ingila

Siyasa
Britain's Prime Minister and Conservative Party leader Rishi Sunak reacts after bowling a ball during a Conservative general election campaign event at the Market Bosworth Bowls Club in Market Bosworth, central England, on May 28, 2024. (Photo by Alastair Grant / POOL / AFP) Firai kinistan Ingila, Rishi Sunak ya bayyana cewa, ba lallai sai mutum na da karatun boko bane zai yi nasara a rayuwa. Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta. Screenshot Saidai lamarin ya jawo cece-kuce sosai inda wasu suka goyi bayansa, wasu kuma suka ce hakan ba daidai bane.
Gwamnatin tarayya ta samo bashin Dala Miliyan dari biyar($500 million) dan gyaran wutar Lantarki

Gwamnatin tarayya ta samo bashin Dala Miliyan dari biyar($500 million) dan gyaran wutar Lantarki

Siyasa
Gwamnatin tarayya ta ciwo bashin dala Miliyan dari biyar, $500 million dan karfafawa kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasa. Hukumar BPE tace an ciwo bashinne dan magance matsalolin da suka mamaye kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasarnan. Wakiliyar hukumar BPE, Amina Othman ce ta bayyana haka inda tace za'a yi amfani da kudadenne wajan sayo mitocin wuta da sauransu.
Hoto: Dansanda ya kash-she wannan matashin saboda yaki bashi cin hancin Naira 200

Hoto: Dansanda ya kash-she wannan matashin saboda yaki bashi cin hancin Naira 200

Tsaro
Ana zargin 'yansanda sun kashe wannan mutumin me shekaru 40 a titin Azikoro Road dake Yenagoa ta jihar Bayelsa saboda yaki bada cin hancin Naira dari biyu(200). Rahoto ya bayyana cewa, mutumin me suna Benalayefa Asiayei yana kan hanyarsa ta komawa gidane daga wajan aiki da misalin karfe 8 na yamma yayin da aka kasheshi. Bayan da 'yansandan suka kasheshi, sun tsere daga wajan amma wani daga cikin shaidun abinda ya faru sun dauki hotunansu. Kakakin 'yansandan jihar, Musa Mohammed ya tabbatar da faruwar lamarin kuma yace sun tantance wanda ake zargi. Iyalan mamakin sun ce suna neman adalci.
Idan muna neman kuri’a mukan je wajan mutane amma da munci zabe sai mu koma Abuja>>inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Idan muna neman kuri’a mukan je wajan mutane amma da munci zabe sai mu koma Abuja>>inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Siyasa
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana damuwa kan halin 'yan siyasa na mantawa da mutane idan suka ci zabe. Ya bayyana hakane ranar Alhamis a yayin ganawa da dattawan Arewa na kungiyar ACF bayan ziyarar da suka kai masa fadarsa. Yace da mun ci zabe sai mu koma Abuja amma idan muna neman kuri'a mukan je gurin mutane. Tinubu ya bayyana muhimmancin ganin cewa, gwamnatocin kananan hukumomi na aiki yanda ya kamata. “People reside in the local communities. That is where they work, farm, and live. If the local governments are not effective in delivering services; as leaders, we must not hang on to the numbers.“Maybe we should look at recalibrating. What was good four years ago may not be good today. When we want the votes, we go to the locals; when we get the votes, we move to an...
Kotu ta samu Donald Trump da laifukan tuhume-tuhume 34 da ake masa

Kotu ta samu Donald Trump da laifukan tuhume-tuhume 34 da ake masa

Siyasa
Tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya zamo shugaban Amurka na farko da za a yankewa hukunci a kan tuhuma ta mugun laifi, bayan da masu taimaka wa alkali yanke hukunci suka same shi da laifi a tuhume-tuhume 34 da ake yi masa. Dukkan tuhume-tuhumen na da alaka da karyar da ya yi a harkokin kasuwancinsa domin boye kudin da ya bayar na toshiyar baki a kan alakarsu da mai fitowa a fina-finan batsa wato Stormy Daniels a lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasar a 2016. Da yake Magana a wajen kotun da ke Manhattan bayan samunsa da laifi, Donald Trump, wanda za a yankewa hukunci a watan Yuli mai zuwa, ya kira sakamakon zaman da aka yi a matsayin an yi masa almundahana da coge kuma hakan wani babban aibune. Sannan ya kara da cewa al’umma za su yanke hukunci na gaskiya a ranar za...
Al’umma na tserewa daga ƙauye a Borno saboda barazanar ISWAP

Al’umma na tserewa daga ƙauye a Borno saboda barazanar ISWAP

Borno, Tsaro
Mayaƙan ISWAP sun bai wa mazauna Kukawa lga sanarwar su bar kauyensu ko kuma su fuskanci kisa kwanaki huɗu da kashe masunta goma sha biyar a yankin Tumbun Rogo. Wani mazaunin garin da ya gudu daga al’ummarsa zuwa Maiduguri sa’o’i uku da samun wannan barazana, ya bayyana hakan ga gidan talabijin na Channels. A yayin da ya ke bayar da labarin yadda lamarin yake, mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa mayakan sun tara jama’ar al’umma daban-daban a ƙaramar hukumar da sanyin safiyar Alhamis, inda suka ce su bar gidajensu kafin ranar Asabar, in ba haka ba za a kashe su. A cewarsa, bayan da suka samu barazanar ‘yan ISWAP din, al’ummomin suka fara barin yankunansu, yayin da wasu suka tafi Kross Kauwa, wasu kuma suka tafi Monguno. Kukawa lga ƙaramar hukuma ce a gefe...
Harin Amurka da Birtaniya ya kashe mutum 14 cikin dare a Yemen

Harin Amurka da Birtaniya ya kashe mutum 14 cikin dare a Yemen

Tsaro
Gidan talabijin na Yemen da ke ƙarƙashin jagorancin ƴan Houthi ya ruwaito cewa an kashe mutum 14 ckin dare, yayin da aka jikkata mutum sama da 30 a lokacin wani hari ta sama da dakarun hadin gwiwa na Amurka da Birtaniya suka ƙaddamar. Cibiyar da ke bai wa dakarun Amurka umurni ta tabbatar da kai harin wanda ta ce na ramuwar gayya ne kan mayaƙan Houthi da ke kai hare-hare a kan jiragen ruwa masu sufuri ta tekun Bahar-maliya, lamarin da ke haifar da tsaiko wajen shigi da ficen kaya a duniya. Cibiyar ta ce makaman da ta harba sun faɗa kan inda suka ƙuduri kai harin guda 13, yayin da aka daƙile harin jiragensu marasa matuƙa takwas. A ƴan watannin nan mayaƙan Houthi na kai hare-hare cikin tekun Bahar-maliya, tekun da ake amfani da shi wajen jigilar kaya a fadin duniya, harin da suka ce...
‘Yansanda a jihar Anambra sun kashe daya daga cikin ‘yan IPOB da suka tursasa mutane su zauna a gida

‘Yansanda a jihar Anambra sun kashe daya daga cikin ‘yan IPOB da suka tursasa mutane su zauna a gida

Tsaro
'Yansanda sun kashe daya daga cikin masu tursasawa mutane zama a gida. An yi bata kashine tsakanin 'yansandan da mutanen wanda aka kashe daya, sauran suka tsere. Hukumar 'yansandan tace lamarin ya farune ranar 30 ga watan Mayu. Kuma ta kwace Bindiga kirar gida daga hannun daya daga cikin 'yan ta'addan inda sauran suka tsere, kamar yanda kakakin 'yansandan jihar, SP Tochukwu Ikenga ya tabbatar.