Saturday, April 26
Shadow

Faduwar da Tinubu yayi zata iya faruwa akan kowa, Cewar Sheikh Pantami, saidai da yawa sun sokeshi akan bai ce komai ba kan kashe-kashen da ake a Arewa amma gashi yana kare shugaban kasa

Babban malamin Addinin Islama, sheikh Isa Ali Pantami ya yi martani kan faduwar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yayi a wajan bikin ranar dimokradiyya.

Sheikh Pantami ya bayyana cewa, faduwar shugaban kasar bata da alaka da shugabanci kuma zata iya faruwa akan kowa. Ya bayar da shawarar cewa a rika kawar da akai akan irin wadannan labarai zai fi kyau.

“This can happen to any of us. It has nothing to do with governance. The earlier we ignore this kind of news, the better. May the Almighty make Nigeria a better place for us.”

Malam yayi martanine bayan da jaridar Vanguard ta wallafa labarin faduwar shugaban kasar.

Karanta Wannan  Hotuna: Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Karbi Bakuncin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai A Gidansa Dake Daura Jihar Katsina, Yau Lahadi

Saidai malam ya sha martani daga bakin wasu dake cewa bai yi magana akan kashe-kashen da akw yi a Arewa ba amma gashi yana kare shugaban kasa.

Waspapping dake amfani da sunan Sarki, wanda ya shahara wajan bayyana ra’ayi da kare muradun Arewa a Twitter ne ya fara magana inda yace cewa an kashe mutane 50 a Kankara amma malam bai yi magana ba sai akan faduwar shugaban kasa.

Karanta Wannan  Hotunan Yadda Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari Ya Gudanar Da Sallar Idin Babbar Sallah A Mahaifarsa, Garin Daura Jihar Katsina, Yau Lahadi

Ya kara da cewa irin su Sheikh Pantami ne ya kamata ace suna kare muradun ‘yan Arewa.

“By the way, I don’t recall seeing a tweet from this man about the killing of 50 farmers in Katsina yesterday, but he has time to tweet about President Bola Ahmed Tinubu falling down.

These are the people who are supposed to speak in our interest.”

Wani me suna Ukasha Abdul Usman ya goyi bayan Waspapping da cewa:

Wani me sunan AK shima yace mutane 50 aka kashe amma baka yi kuka ba malam:

Karanta Wannan  Lokacin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na gwamnan Kaduna an cire Naira Biliyan 423 daga asusun bankin jihar ba tare da yin wani aiki da kudin ba>>Majalisar Jihar
https://twitter.com/HassanHusseinY1/status/1800913523813331126?t=urp_S71_IrD1lM6CgZEG4w&s=19

Me zaku ce?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *