Monday, June 29
Shadow

Duk Labarai

Yawan wanda suka mutu bayan harin kunar bakin wake sun kai 30, guda 100 sun jikkata a jihar Borno

Yawan wanda suka mutu bayan harin kunar bakin wake sun kai 30, guda 100 sun jikkata a jihar Borno

Borno, Tsaro
Rahotanni daga jihar Borno na cewa, yawan wadanda suka mutu ya karu zuwa 30 daga 8 da jami'n tsaro suka bayyana a jiya. Hakanan yawan wadanda suka jikkata ya karu zuwa 100. Rahoton jaridar Vanguard ya ruwaito cewa, sarkin Gwoza, Alhaji Mohammed Shehu Timta ya tabbatar da faruwar lamarin. Jaridar tace Timta ya bayyana mata cewa 'yar kunar bakin wake ta farko ta je wajan bikine tare da yara inda ta tayar da bam sannan an samu ta biyu itama taje wajan wani bikin ta sake tayarwa. Timta ya kara da cewa, an sake samun wani tashin bam din a karo na 3. A baya dai, jaridar Premium times ta ce 'yan kunar bakin wake 4 ne suka tayar da bamabamai a Garin na Gwoza. Timta dai yace ba'a kammala samun bayanai ba amma zuwa yanzu mutum 100 sun jikkata kuma an garzaya da wasu zuwa Maiduguri.
Bayan Awa 24 da yin Gàrkùwà da magaifiyar Rarara har yanzu ba’a gano inda take ba

Bayan Awa 24 da yin Gàrkùwà da magaifiyar Rarara har yanzu ba’a gano inda take ba

Katsina, Rarara, Tsaro
Rahotanni sun bayyana cewa, awanni 24 bayan yin garkuwa da mahaifiyar shahararren mawakin siyasa, Dauda Adamu Kahutu, Rarara har yanzu, ba'a gano inda take ba. Kakakin 'yansandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya bayyana cewa an kama mutane 2 da ake zargin suna da hannu a yin garkuwa da mahaifiyar Rarara din amma har yanzu ba'a gano inda take ba. Daily Trust ta ruwaito cewa 'yan Bindigar da suka je yin garkuwa da mahaifiyar Rarara sun je ne a kafa tike da muggan makamai suka shiga gidanta suka kamata. Rahoton yace Bata musu gaddama ba kuma babu wanda ya tunkaresu saboda muggan makaman da suke dauke dasu. Daily Trust tace ta nemi jin ta bakin Rarara amma bata yi nasara ba saboda wayoyinsa duk a kulle kuma an aika masa da sakon waya amma bar bayar da amsa ba.
Ba’a taba shugaban kwarai mutumin arziki iin Tinubu ba>>Kashim Shettima

Ba’a taba shugaban kwarai mutumin arziki iin Tinubu ba>>Kashim Shettima

labaran tinubu ayau, Siyasa
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaban da ba'a taba yin irinsa ba wajan jajircewa da yiwa Najeriya aiki. Ya bayyana hakane jiya kamar yanda jaridar thisday ta bayyana. Yace shugabanci ba da karfin jiki ake yinsa ba, da kaifin tunani ake yinsa dan haka a daina alakanta lafiyar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da shugabancin da yake. Ya kuma yi Allah wadai da wadanda suka rika yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dariya a ranar Dimokradiyya data gabata.

Harin kunar bakin wake ya kashe mutane 8 a Maiduguri da jikkata wasu da dama

Borno, Tsaro
Rahotanni daga jihar Borno na cewa harin Bom ya kashe akalla mutane 8 da jikkata mutane da dama. Harin wanda na kunar bakin wakene mahara 4 ne suka kaishi kuma rahoto yace dukansu sun mutu. Hukumar 'yansandan jihar ta tabbatar da mutane 8 ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata. Kakakin 'yansandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso ya bayyana cewa lamarin ya farune da misalin karfe 3:40 na safiyar yau,Rabar, 29 ga watan Yuni. Rahoton yace wata mata dake goye da yaro ta tayar da bom din a tashar motar Mararraba dake T. Junction dake garin Gwoza. Matar da dan da take goye dashi da wasu 6 sun mutu. A bangaren jaridar Premium times kuwa, tace mata 4 ne suka tayar da bamabamai a bangarori daban-daban na jihar wanda yayi sanadiyyar mutuwar mutanen da ba'a kai ga tantance yawansu ba c...
DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin cire kowanne irin haraji akan magunguna da kayan asibiti da ake shigowa da su ƙasar nan

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin cire kowanne irin haraji akan magunguna da kayan asibiti da ake shigowa da su ƙasar nan

labaran tinubu ayau, Siyasa
Cire harajin ya shafi kayan asibiti da suka haɗa da magunguna na ƙwayoyi da na ruwa, sirinji da allurai, sanke na rigakafin cizon sauro, abubuwan gwaji na gaggawa, da sauran kayan amfani a asibiti na yau da kullum. Hakazalika, umarnin na shugaban ƙasa zai ƙara ƙarfafawa masana'antun sarrafa magunguna da kayan asibiti na cikin gida wajen kara inganta su da samar da su a wadace. Wannan zai rage farashin magunguna da kuma wadatar su a lunguna da saƙon kasar nan don amfanin ƴan Najeriya.
“Idan Aka Kira Ni Naje Aso Villa a Matsayin Uwargidan Shugaban Kasa Ba Zan Je Ba” – Patience Jonathan

“Idan Aka Kira Ni Naje Aso Villa a Matsayin Uwargidan Shugaban Kasa Ba Zan Je Ba” – Patience Jonathan

Siyasa
Uwargidan tsohon shugaban kasa, Dame Patience Jonathan ta ce idan aka bukaci ta koma fadar shugaban kasa ta yi aiki a matsayin uwargidan shugaban Najeriya, za ta ki ba zata jeba. A cikin wani faifan bidiyo na Misis Patience, wacce ta yi magana a ranar Juma'a a wurin wani taron jama'a, ta ce " damuwar Najeriya ta yi yawa", tana mai jaddada cewa ta yi kasa da lokacin da take kan mulki. A cewarta, “Idan kun kira ni yanzu don naje villa, ba zan je wurin ba. Ba zan yi ba. Ba ku ga yadda nake matashiya ba? Damuwar tana da yawa. “Matsalar Najeriya ta yi yawa. Idan Allah Ya yi nasarar fitar da ku daga cikinta, to ku tsarkake Shi. Ya kai ka can sau ɗaya, me yasa kake son komawa can kuma”? Dimokuradiyya ta rahoto cewa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fice daga fadar shugaban ka...

Ƴań Bìñďîģà Sun Sácé Mąhaifiýar Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara A Gârin Kahutu Dáke Ƙaramar Hukumar Dánja, Jihar Kátsina A Darén Jiya Al-hamis

Tsaro
Ƴań Bìñďîģà Sun Sácé Mąhaifiýar Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara A Gârin Kahutu Dáke Ƙaramar Hukumar Dánja, Jihar Kátsina A Darén Jiya Al-hamis Allah Ya Bayyana Ta Cikin Aminci. An baza jami'an tsaro na zuwa dazukan jihar Katsina dòmin su kubutar da mahaifiyar mawaƙi Dauda Rarara kamar yadda rundunar ƴansandan jihar Katsina ta bayyana Allàh ya bayyana ta. Ina Roƙon Ƴan Uwa Músúlm Da Ku Taya Ni Da Addu'ar Allâh Ya Kuɓutar Da Mahaifiyata, Ta Dawo Gida Cikin Ƙoshin Lafiya, Roƙon Mawaƙi Rarara Ga Al'ummar Nájeriya Allah Ya bayyana ta.
El-Rufa’i ya maka majalisar dokokin Kaduna a kotu

El-Rufa’i ya maka majalisar dokokin Kaduna a kotu

Kaduna, Siyasa
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya shigar da ƙara a gaban kotu, inda yake ƙalubalantar majalisar dokokin jihar kan zarge-zargen da ta yi masa na almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin mulkinsa. Gwamnan ya shigar da ƙarar ne a ranar Laraba a wata babbar kotun tarayya da ke birnin Kaduna. Wata sanarwa da tsohon gwamnan ya fitar ta hannun mai ba shi shawara kan yaɗa labaru, Muyiwa Adekeye, ta ce Elrufa'i ya shigar da ƙarar ce domin tabbatar da haƙoƙoƙin da yake da shi na kare kai game da binciken da majalisar dokokin jihar ta ce ta yi a kansa. Lauyan El-Rufa'i, AU Mustapha ya ce tsohon gwamnan ya ɗauki matakin ne ganin cewa yana da hakkin a saurare shi a duk wani mataki na bincike ko kotu da za a ɗauka kansa, kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada. Sabod...
Kalli Yanda sojojin kasar Yahudawan Isàèlà ke taka tutar kasar Saudiyya

Kalli Yanda sojojin kasar Yahudawan Isàèlà ke taka tutar kasar Saudiyya

Siyasa
An ga wani hoto dake nuna sojojin kasar Yahudawan Israela suna taka tutar kasar Saudiyya me dauke da kalmar shahada. Lamarin ya jawo tayar da jijiyoyin wuya matuka inda da dama suka ce dama addinin musulunci ne kasar Israelan take yaka ba kasar Palasdinawa ba kadai. Wasu dai na zargin kasar Saudiyya da kin daukar matakan da suka dace dan baiwa palasdinawa kariya daga kisan da kasar Israela take musu.