An hangi sojan Ruwa, AM. Yerima a wajan wani Bikin Kirsimeti da aka yi a Abuja.
Mutane da yawa sun ji dadin ganinsa a wajan.
Wasu masu wasan Barkwanci a wajan an ga suna tsokanarsa.
https://twitter.com/Cleverlydey4u/status/2004458666003673456?t=RRcLTUOY4cEK2xVPQxRs8Q&s=19
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, tun tuni ya kamata ya kai Najeriya hari, watau Rana Laraba.
Amma yace ya jinkirta sai ranar Kirsimeti ne dan harin ya zama waa kyauta ta musamman.
Ya bayyana hakane ranar Laraba, Kwana daya bayan kai harin Sokoto da Kwara wanda rahotanni suka ce ba kan 'yan Tà'àddà ya fada ba.
Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, harin da kasar Amurka ta kawo Najeriya bata yi kokari ba.
Yace Sojojin Najeriya na da kwarewa da makaman da zasu iya kai irin wannan hari.
Yace Yana kiran Gwamnati ta yanke hulda da Amurka sannan kuma idan taimakon yaki da ta'addanci take nema ta nema wajan kasashen Pakistan, Turkiyya ko China.
Yace dalili kuwa shine shugaban kasar Amirka, Donald Trump a wulakance yake kallon Najeriya
Wasu hotuna da Bidiyon AI sun watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka hada Hadiza Gabon da Adam A. Zango dake nuna alamar sun soyayya.
A baya dai Masoyan Adam A. Zango sun nuna fushi kan rashin saka hoton sa a dakin da Hadiza Gabon ke Hira da mutane.
Hakan ya dumama kafafen sadarwar Arewa sosai.
Danna Nan dan kallon Bidiyon
An ga Me baiwa shugaban kasa shawara akan Harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu suna a cikin mota daya tare da shugaban kasa.
Hakan yasa mutane ke ta maganganun cewa, lamarin tsaro ne suka tattaunawa shiyasa.
https://twitter.com/DejiAdesogan/status/2004655440043671604?t=n1OFHqTh422CKlyKnPTE1w&s=19
Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar ya bayyana cewa harin da Amurka ta kawo Najeriya ba shine na karshe ba.
Yace akwai yiyuwar irin wadannan hare-haren anan gaba.
Yace Najeriya suna hada kai da duk wata kasa da zata taimaka mata wajan yakar ta'addanci
https://twitter.com/trigottista/status/2004483596648956302?t=E56lwh6m-vI2uA9DI4z0lg&s=19
Majiyoyi da suka haɗa da na gwamnatin jihar Kwara sun tabbatar da cewa an kai harin a wani ƙauye da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Offa, inda a ƴan kwanaki wasu ƴan bindiga suka kai hari a coci wanda ya yi sanadiyya rasa ran mutum biyu sannan suka yi awon gaba da dama.
Hotuna da BBC ta samu daga mazauna garin sun nuna yadda makamin ya faɗa kan gidajen al'umma a garin Offa inda ya rugurguza katangun wasu tsirarun gine-gine.
Wani jami'in gwamnati ya ce al'amarin ya faru a wurare da dama a cikin garin na Offa da suka hada da filin Idi da wasu otal guda biyu da suka hada da Offa Central hotel da Solid Worth Hotel
Sojan Najeriya ya godewa Kasar Amurka kan harin data kawo Najeriya.
Yace suma yanzu zasu samu saukin yaki da suke da Tshàgyèràn Dhàjì.
https://twitter.com/General_Somto/status/2004476880179827086?t=wtXfuR8kZNkNqwpbMHH9AQ&s=19
A daren jiya ne dai kasar Amurka tace ta kai Khàrì kan tshageran Dhajin a jihar Sokoto.
HARE-HAREN AMURKA A SOKOTO: Ba mafakar ’yan ta’adda aka kai wa hari ba kusa da Asibiti harin ya fada –inji Dan Majalisar yankin Hon. Bashar Isah
Daga Ayau News
Dan Majalisar Dokokin Jihar Sokoto mai wakiltar Tambuwal ta Gabas yankin da abun ya faru, Hon. Bashar Isa Sarkin Yakin Jabo, ya musanta ikirarin cewa akwai mafakar ’yan ta’adda a yankin Jabo, inda aka ce sojojin Amurka sun kai hari a daren Alhamis.
Ayau News ta ruwaito a hirarsa da DCL, Hon. Bashar ya ce wurin da abin ya faru kusa da Asibitin Jabo PHC ne, yankin da al’umma ke zaune lafiya, ba cikin daji ba, kuma babu wani bayani da ke nuna ayyukan ’yan ta’adda a yankin.
Ya kara da cewa bayan harin, jama’ar yankin na cikin fargaba da tsoro, ganin cewa ba su san inda abin makamancin haka zai sake faruwa ba. Ya jaddada ...