Friday, April 24
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon wasan Najeriya da Morocco a kasar Morocco yace ‘yan Najeriya a filin wasan basu wuce su 20 ba, da ace Najeriya taci Morocco da sun dandana kudarsu

Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon wasan Najeriya da Morocco a kasar Morocco yace ‘yan Najeriya a filin wasan basu wuce su 20 ba, da ace Najeriya taci Morocco da sun dandana kudarsu

Duk Labarai
Wani dan Najeriya da ya je kasar Morocco kallon wasan Najeriya da Morocco ya dauki hankula bayan da yace duka 'yan Najeriya da suka je filin wasan basu wuce su 20 ba. Yace da Najeriya ta ci Morocco, da sun dandana kudarsu. https://twitter.com/i/status/2011684491723751586
Mawakin Najeriya, Davido ya tafka Asarar Naira Miliyan 495 a cacar da ya buga cewa Najeriya ce zata yi nasara a wasanta da Morocco

Mawakin Najeriya, Davido ya tafka Asarar Naira Miliyan 495 a cacar da ya buga cewa Najeriya ce zata yi nasara a wasanta da Morocco

Duk Labarai
Shahararren mawakin Najeriya, Davido ya bayyana cewa ya tafka asarar Naira Miliyan 495 saboda cacar da ya buga akan cewa Najeriya ce zata ci Morocco. Davido dai wanda yayi suna wajan yin caca da son kwallo, ya saka cewa, Najeriya ce zata ci amma sai Morocco ta yi nasara. Davido ya wallafa rasit din cacar da yayi a shafinsa na sada zumunta.
Ji abinda Mataimakin Gwamnan Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo yayi kan komawar Abba Kabir Yusuf APC da ya jawo masa yabo

Ji abinda Mataimakin Gwamnan Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo yayi kan komawar Abba Kabir Yusuf APC da ya jawo masa yabo

Duk Labarai
Mataimakin Gwamnan jihar Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo ya bayyana goyon baya ga Kwankwaso a bayyane a yayin da Gwamna, Abba Kabir Yusuf ke shirin komawa APC. An ga Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo a gidan Kwankwaso ranar Laraba a yayin da wasu 'yan kwankwasiyyar suka kaiwa Kwankwaso ziyara a gidansa dake Kano. Ya zauna a kusa da Kwankwaso yayin ganawar wanda da yawa 'yan Kwankwasiyya suka bayyana cewa hakan alamar nuna yana tare da Kwankwaso ne.
Gwamnatin tarayya ta sanar da sabon harajin VAT da ‘yan Najeriya masu amfani da banki zasu biya

Gwamnatin tarayya ta sanar da sabon harajin VAT da ‘yan Najeriya masu amfani da banki zasu biya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bukaci bankuna su fara karbar sabon Harajin VAT na kaso 7.5 akan duk wani amfani da masu hulda da banki suke yi. Za'a rika cire harajinne akan aika kudi, karbar katin ATM, duba balance da sauransu. Kuma Harajin zai fara aiki ne nan da ranar 19 ga watan Janairu, watau Ranar Litinin me zuwa. Tuni dai bankunan suka aikawa masu hulda dasu sanarwar fara karbar Haraji.