
Bayan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai da babbar kotun tarayya dake da zama a Kaduna ta yi, ta saka masa sharuda.
Sharadi na farko shine an bayar da belin nasa akan Naira Miliyan 200.
Sannan an saka masa dokar kada ya sake yayi hira da wata kafar yada labarai.
A yau ne dai kotun ta bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan da ya shafe kwanaki a tsare.
Saidai har yanzu babbar kotun jihar Kaduna bata bayar da belin nasa ba inda tace sai ranar 21 ga watan Afrilu.