Wednesday, August 19
Shadow

Gwamnatin tarayya ta bude sabbin tashoshin talabijin 100 da ‘yan Najeriya zasu rika kallo Kyauta

Gwammatin tarayya na sanar da bude gidajen talabijin 100 da ‘yan kasa zasu rika kallo kyauta ba tare da biyan kudi duk wata ba.

A jumlace an musu sunan FreeTV.

Fadar shugabab kasa ce ta sanar da wannan a ranar Laraba.

Sanarwar tace gidajen Talabijin din sun hada dana labarai dana wakoki dana wasannin yara dana ilimi a ciki da wajen Najeriya.

Sanarwar tace wannan mataki ne na inganta kafofin watsa labarai zuwa na zamani.

Karanta Wannan  Ana ta kiran a kama wasu matasa da suka fito Zàngà-zàngà suna nuna cewa shugaba Tinubu na da hannu a matsalar tsaro

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *