
Gwammatin tarayya na sanar da bude gidajen talabijin 100 da ‘yan kasa zasu rika kallo kyauta ba tare da biyan kudi duk wata ba.
A jumlace an musu sunan FreeTV.
Fadar shugabab kasa ce ta sanar da wannan a ranar Laraba.
Sanarwar tace gidajen Talabijin din sun hada dana labarai dana wakoki dana wasannin yara dana ilimi a ciki da wajen Najeriya.
Sanarwar tace wannan mataki ne na inganta kafofin watsa labarai zuwa na zamani.