
Fadan cacar baki ya barke tsakanin Magoya bayan Sheikh Farfesa Hon. Isa Ali Pantami da Malam Albanin Gombe.
Albanin Gombe ya kawo misalai na yanda Jamilu Gwamna ke taimakon jama’a inda yace Marigayi Sadiq Pharmacy ana binsa bashin Naira Miliyan 8.
Yace Jamilu Gwamna ne ya bayar da tallafin Naira Miliyan 3 yace a ragewa mamacin bashin.
Ya sakawa Farfesa Isa Ali Pantami sunan dan iya, inda yace babu abinda yakewa jama’a.
Sannan Albanin Gombe yace idan aka kaishi bango Akwai wasu sirrika da zai Tona.