
Masoyan Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango sun sha Alwashin sai masa fom din takarar gwamna ko dan majalisa a jihar Kaduna.
Sun kuma sha alwashin tsayawa dan yi masa yakin neman zabe.
Saidai a martaninsa, Adam A. Zango yace shi yana tare da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima amma ya gode da soyayyar da masoyan nasa suka nuna masa.