
Anisee yace wai idan Anje Ranar Lahira sai Shehu Ibrahim yace a kawo masa ‘yan Izala, sai ‘yan Faila suce Shehu ai ‘yan Faila ne naka ya zakace a kawo maka ‘yan Izala?
Sai Shehu yace shi dai a kawo masa ‘yan Izala
Idan aka kawo masa ‘yan Izala, suna zuwa gabansa suka zauna sai su fashe da kuka, shima shehu sai ya fashe da kuka.
Sai Shehu ya tambayesu kukan me suke?
Sai suce da sun san haka soyayyar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) take da dadi da sun saurari shehu a yayin da yake kiransu zuwa gareta.
Sai su kuma suce Ne yasa shehu yake kuka?
Sai yace shi kuma yana kuka ne yana jimamin kada Allah ya tuhumeshi akan rashin karbar soyayyar manzon Allah da ‘yan Izala basu yi ba saboda shi Allah ya baiwa kwangilar yada soyayyar Allah.
