Tuesday, May 27
Shadow

Na yi nadamar yiwa Tinubu yakin neman zabe, Jama’a ku yafe min kan jawo hankalinku da na yi kuka zabeshi>>Dan Balki Kwamanda

Dan siyasa a jiar Kano, Dan Balki Kwamanda ya bayyana nadama kan jawo hankalin mutane da yayi suka zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaban kasa.

Yace yayi nadamar yakin neman zaben da yawa Tinubu.

Yace tunda yake a rayuwarsa bai taba yin abinda yayi nadamarsa sosai ba kamar yiwa Tinubu yakin neman zabe.

Yace dalili kuwa shine alkawuran da Bola Ahmad Tinubu ya dauka be cika ba kuma mutane na cikin matsananciyar wahala.

Ya bayyana hakane a watan hira da gidan Jaridar Daily Trust suka yi dashi inda yace yana neman yafiyar wadanda ya yaudara.

Karanta Wannan  An min Wahayi cewa nan gaba a saman wata da kuke gani a sama zamu je mu yi zaman taro>>Inji Pastor Enoch Adeboye

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *