Monday, December 15
Shadow
Babu kotun da ke da hurumin tursasa mutane su yi aure dole>>Inji Kungiyar Lauyoyi ta kasa, NBA akan maganar auren Maiwushirya da ‘YarGuda

Babu kotun da ke da hurumin tursasa mutane su yi aure dole>>Inji Kungiyar Lauyoyi ta kasa, NBA akan maganar auren Maiwushirya da ‘YarGuda

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA ta fitar da matsaya game da auren 'YarGuda da Maiwushirya. Kungiyar tace ta samu labarin auren wanda wata kotun Magistrate ta yi a Kano. Tace babu wata kotu dake da hurumin tursasa mutum yayi aure saboda hakan take hakkin bil'adama ne saboda aure abune wanda mutum ke yi saboda akwai soyayya da fahimtar juna tsakanin masoyan. Dan haka NBA tace tana neman a sake duba wannan hukunci dan tabbatar ba'a takewa wanda lamarin ya shafa ba hakkinsu. Saidai Rahotanni sun nuna cewa, Maiwushirya da kanshi ne yace zai auri 'YarGuda inda itama ta amince da hakan.
Kalli Bidiyon Yanda wata sabuwar Dirama ta sake faruwa tsakanin Sanata Natasha Akpoti da Kakakin majalisa, Godswill Akpabio a zauren majalisar

Kalli Bidiyon Yanda wata sabuwar Dirama ta sake faruwa tsakanin Sanata Natasha Akpoti da Kakakin majalisa, Godswill Akpabio a zauren majalisar

Duk Labarai
Wata sabuwar dirama tsakanin Kakakin Majalisar Dattijai Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti ta faru a zaman majalisar. Ana karanta wata sabuwar doka ce akan zubar da ciki amma akan jinginar da dokar dan sake dubata. Bayan Godswill Akpabio ya sanar da dakatar da tattauna kudirin dokar, Sanata Natasha ta nemi a bata damar yin magana akan kudirin. Saidai sauran sanatoci sun ce bata damar maganar bayan dakatar da tattauna kudirin ya sabawa dokar majalisar. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1980710412988608574?t=mvl9_YCql2eL8AL0LIQWgQ&s=19
Kalli Bidiyo Da Duminsa: A karshe dai an baiwa Maiwushirya kyautar gida saboda ‘YarGuda tace ba zata aureshi ba sai yana da gida

Kalli Bidiyo Da Duminsa: A karshe dai an baiwa Maiwushirya kyautar gida saboda ‘YarGuda tace ba zata aureshi ba sai yana da gida

Duk Labarai
Wani me suna Uban Harkallah yawa Maiwushirya alkawarin gida kyauta amma yace kusa da ofishin Hisbah. Yace dalilinsa shine ya ji 'yar Guda tace ba zata auri Maiwushirya ba sai yana da gida. Yace dan haka ya bashi kyautar wannan gida halas malas yace ya je ya karbi takardun gida. https://www.tiktok.com/@hafizuuba/video/7563663525223140626?_t=ZS-90kAhWy5UTx&_r=1
Kalli Bidiyo: ‘YarGuda tace ba zata bari Maiwushirya ya kara aure ba, daga ita an kulle kofa

Kalli Bidiyo: ‘YarGuda tace ba zata bari Maiwushirya ya kara aure ba, daga ita an kulle kofa

Duk Labarai
Amaryar Maiwushirya, 'YarGuda tace ba zata bari ya kara aure ba. Tace daga ita an kulle kofa. Ta bayyana hakane a wani Bidiyon ta da ya watsu sosai inda aka ganta ana mata tambayoyi. https://www.tiktok.com/@pharooq_/video/7563708394104818965?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7563708394104818965&source=h5_m&timestamp=1761076676&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7559465894419449601&share_link_id=43f8e117-d4b6-4179-8262-9418d7256029&share_app_id=1233&ugbiz_name=MAIN&...
Kalli Bidiyon: Ango Maiwushirya ya kwanta rashin lafiya, wasu na cewa zullumin Auren Wada ne ya kwantar dashi

Kalli Bidiyon: Ango Maiwushirya ya kwanta rashin lafiya, wasu na cewa zullumin Auren Wada ne ya kwantar dashi

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Maiwushirya ya kwanta rashin lafiya kwana daya bayan da aka ce a daura masa aure da wada wadda aka fi sani da 'YarGuda da suke Bidiyo da ita. An ga dai ana masa karin ruwa yayin da yake kwance akan gado. Wasu sun rika masa fatan samun sauki inda wasu ke cewa zullumin auren wada ne ya sashi gaba. https://www.tiktok.com/@pharooq_/video/7563677050993708309?_t=ZS-90k0eoezJtR&_r=1
Gwamnati ta kwace gidan dala Miliyan $2.5 da tsohon ma’aikacin kamfanin mai na kasa, NNPCL, Paulinus Iheanacho Okoronkwo ya siya da kudin sata a kasar Amurka

Gwamnati ta kwace gidan dala Miliyan $2.5 da tsohon ma’aikacin kamfanin mai na kasa, NNPCL, Paulinus Iheanacho Okoronkwo ya siya da kudin sata a kasar Amurka

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta kwace gidan Dala Miliyan $2.5 da tsohon ma'aikacin kamfanin mai na kasa, NNPCL, Paulinus Iheanacho Okoronkwo ya siya a kasar Amurka da kudin sata. A watan Augusta ne aka yanke masa hukuncin daurin shekaru 30 a gidan yari bayan samunsa da laifin rashawa da cin hanci. An sameshi da laifin karbar cin hanci har dala Miliyan $2.1 daga wani kamfanin mai me suna Addax Petroleum da zummar cewa zai samarwa da kamfanin lasisin hakar danyen man fetur a Najeriya. Kuma ya sayi gidanne a Valencia dake California kasar Amurka.
Kalli Bidiyon mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima yana cewa, ‘Yan Najeriya kun yi sa’a da Allah ya baku ni a matsayin mataimakin shugaban kasa

Kalli Bidiyon mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima yana cewa, ‘Yan Najeriya kun yi sa’a da Allah ya baku ni a matsayin mataimakin shugaban kasa

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun taki sa'a da Allah ya basu shi a matsayin mataimakin shugaban kasa. Ya bayyana hakane a ziyarar da ya kai jihar Katsina. Da yake jawabi, Kashim Shettima yace Katsinawa sun yi dace da Allah ya basu Dikko Raddah a matsayin gwamnan, yace a tafa masa. Sannan yace 'yan Najeriya kuma sun yi dace da Allah ya basu shi a matsayin mataimakin shugaban kasa. https://www.tiktok.com/@kashiimshettima/video/7563681781183040776?_t=ZS-90js9tRs0Zd&_r=1