Monday, December 15
Shadow
Da Duminsa: Dangote zai sayar da wani sashe na matatar mansa

Da Duminsa: Dangote zai sayar da wani sashe na matatar mansa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Attajiri, Dangote zai sayar da wani kaso tsakanin kaso 5 zuwa 10 na matatar mansa a kasuwar hannun jarin Najeriya. Dangote ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a kafar  S&P Global ranar 20 ga watan October inda yace zai yi hakanne kamar yanda yawa kamfanoninsa na sukari dana Siminti. Dangote yace baya son rike fiye da kaso 65 zuwa 70 cikin 100 na hannun jarin matatar man. Yace a hankali a hankali zai rika sayar da hannun jarin matatar ya danganta ga yanda mutane ke son saye ko kuma yanayin kasuwa. Hakanan Dangote yace yana son kara yawan man fetur din da suke tacewa duk rana zuwa ganga Miliyan 1.4 a kowace rana. Idan hakan ta tabbata, matatar man Dangote zata zama ta daya a Duniya wajan yawan fitar da man fetur inda zata zarta ta kasar I...
Allah Sarki,Kalli Bidiyo gwanin ban tausai, Sun dauke ta da niyyar aikata Alfasha, Ashe matsayafa ne, duk da tana rokonsu su yi hakuri, sun mata Tsyrara suka aikata inda ba’a dawowa dan yin tsyfin kudi

Allah Sarki,Kalli Bidiyo gwanin ban tausai, Sun dauke ta da niyyar aikata Alfasha, Ashe matsayafa ne, duk da tana rokonsu su yi hakuri, sun mata Tsyrara suka aikata inda ba’a dawowa dan yin tsyfin kudi

Duk Labarai
Wannan wata Budurwa ce da lamarin ta ya baiwa mutane da yawa tausai. Wasu matasa matsafa da aka fi sani da Yahoo Boys ne suka dauketa suka kaita gida da niyyar aikata Alfasha da ita amma a karshe ashe tsafi zasu yi da ita. An ga Bidiyon ta tana ta rokon su kada su Kashye ta amma suka aikata lahira? Suka cire mata kai, da gabanta da sauran wasu sassan jikinta. A karshe dai asirinsu ya tonu an kamasu. Danna nan dan kallon Bidiyon
Kungiyar Malaman Jami’a, ASUU ta janye yajin aikin data shiga

Kungiyar Malaman Jami’a, ASUU ta janye yajin aikin data shiga

Duk Labarai
Ƙungiyar malaman jami’o’in Najeriya ASUU ta dakatar da yajin aikin gargadi na tsawon makonni biyu da ta fara, inda ta bai wa gwamnatin ƙasar wata ɗaya domin ta magance buƙatunta. Shugaban ƙungiyar, farfesa Chris Piwunayayin wata ganawa da manema labarai, ya ce ƙungiyar ta yanke shawarar dakatar da yajin aikin ne domin bai wa gwamnati dama ta nuna kyakkyawan niyya wajen tattauna matsalolin da suka shafi albashi da kayan aiki da inganta yanayin aiki a jami’o’in kasar. Ƙungiyar ta ce abun da yasa suka janye yajin aikin shine gwamnati ta gabatar da matsayarta kan sabunta yarjejeniysar shekarar 2009 kuma da kiraye-kirayen da suka samu daga mutane da dama daga ƙasar domin sun janye yajin aikin. Wannan ne ya sa ƙungiyar ta bai wa gwamnatin ƙasar wata ɗaya domin ta magance buƙatunta. K...
Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Tiktok ko ba zaku iya kama gida a Abuja ba, ko Kaduna ce ku je ku maqale, dan Kano ba wajan zamanku bane>>Gfresh Al-amin

Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Tiktok ko ba zaku iya kama gida a Abuja ba, ko Kaduna ce ku je ku maqale, dan Kano ba wajan zamanku bane>>Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya baiwa 'yan Tiktok dake zaune a Kano shawarar su bar garin. Ya bayyana hakane a Bidiyon daya wallafa bayan sanar da shirin auren Maiwushirya da 'YarGuda. Gfresh yace An fara yiwa maza auren dole inda yace ko ba zasu iya kama gida a Abuja ba ko Kadunane su koma da zama ya fiye musu. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7563781078125710610?_t=ZS-90lCnk8mKbx&_r=1
Matan aure ku rike mazajenku da kyau, Rayuwar Zawarci ba dadi>>Inji wannan Bazawarar

Matan aure ku rike mazajenku da kyau, Rayuwar Zawarci ba dadi>>Inji wannan Bazawarar

Duk Labarai
Wata bazawara daga kudancin Najeriya ta baiwa matan aure shawarar su rike mazajensu da kyau inda tace rayuwar zawarci ba dadi. Bazawarar me amfani da sunan @rhoda2369 a kafafen sada zumunta tace rayuwar aure akwai kalubale amma mata su daure, rabuwa ba itace mafita ba. Tace zata baiwa mace shawarar kashe aurenta ne kawai idan ta samu labarin cewa, ana dukanta.
Kalli Bidiyon: Rigar da diyar Ministan kasar Iyran dake kula da tabbatar da saka hijabi ta saka a wajan Bikinta ta jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Rigar da diyar Ministan kasar Iyran dake kula da tabbatar da saka hijabi ta saka a wajan Bikinta ta jawo cece-kuce

Duk Labarai
Ganin diyar Ministan kasar Iran dake kula da tabbatar da saka Hijabi ta saka riga wadda babu kafada a wajan bikinta ya jawo cece-kuce. Bayyanar Bidiyon a kafafen sada zumunta ya jawo zazzafar Muhawara wanda hakan yasa wasu ke sukar Gwamnatin da munafurci. Shi dai wannan Ministan na kusa ne ga shugaban Jamhuriyar ta Iran. Sunan Ministan Ali Shamkhani kuma a baya shine sakataren Ayatollah Khamenei sannan shine shugaban kula da tabbatar da saka Hijabi a kasar, kamar yanda daily Mail ta ruwaito. A Bidiyon an ganshi tare da diyarsa inda sauran manyan baki a wajan ke musu tafi. Ana dai ganin wannan shigartata ta yi kalar ta kasashen turai wadda kasar Iran ke yaki da irij Al'darsu. https://www.youtube.com/watch?v=lVOJ80OzOTo
Da Duminsa: Kasa da sati daya da bayyanar Rahoton yunkurin yiwa shugaba Tinubu Juhyin Mulki, Gwamnati ta fara maganar yiwa sojojin Najeriya karin Albashi

Da Duminsa: Kasa da sati daya da bayyanar Rahoton yunkurin yiwa shugaba Tinubu Juhyin Mulki, Gwamnati ta fara maganar yiwa sojojin Najeriya karin Albashi

Duk Labarai
Majalisar Dattijai ta nemi a karawa sojojin Najeriya Albashi musamman lura da yanayin tsadar rayuwa da kasarnan ke ciki. Majalisar tace ya kamata a karawa sojojin dake sadaukar da rayuwarsu dan baiwa kasarnan kariya Albashi. Hakannna zuwane kasa da sati daya da bayyanar rahotannin yunkurin juyin mulki da ke cewa an kama sojoji 16 dake da hannu a lamarin.