Monday, December 15
Shadow
Kalli Bidiyon yanda Aka warce wayar wannan Faston a kan Titin Birnin Landan yayin da yake daukar kansa hoton Bidiyo yana addu’a

Kalli Bidiyon yanda Aka warce wayar wannan Faston a kan Titin Birnin Landan yayin da yake daukar kansa hoton Bidiyo yana addu’a

Duk Labarai
Wani fasto me suna Pastor Isaac Anderson’s an warce masa waya akan titin birnin Landan yayin da yake daukar kansa hoto yana addu'a. Faston yace wani ne akan keke ya je ya warce masa wayar wadda yace iPhone 16 pro ce. Saidai yace abinda yafi damunsa shine abubuwan dake ciki. Kalli Bidiyon faruwar lamarin a kasa: https://twitter.com/vanguardngrnews/status/1971310965154312676?t=85aCbjx3K-O1qsthg45IdA&s=19
Kalli Bidiyo: Na yi mamaki da naji ance Kwankwaso zai dawo APC, saboda a baya ya Zhaghi shugaba Tinubu sannan yace masu shiga APC Mahaukata ne>>Inji Ganduje

Kalli Bidiyo: Na yi mamaki da naji ance Kwankwaso zai dawo APC, saboda a baya ya Zhaghi shugaba Tinubu sannan yace masu shiga APC Mahaukata ne>>Inji Ganduje

Duk Labarai
Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana mamakin sa da jin labarin komawar Kwankwaso APC. A wata hira da aka yi dashi bayan taron masu ruwa da tsaki a jam'iyyar APC ta Kano, Ganduje yace Kwankwaso ya yi munanan kalamai na zagi da cin mutunci ga shugaban kasa da jam'iyyar APC amma gashi wai yau shine ke shirin komawa jam'iyyar. Kalli Bidiyon anan: https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1971447796122501280?t=jGM3xeLPD9upzrxQmB7HPA&s=19
Da Duminsa: Kwankwaso ya fara tattaunawa da shugaban jam’iyyar APC a shirin da yake na komawa Jam’iyyar

Da Duminsa: Kwankwaso ya fara tattaunawa da shugaban jam’iyyar APC a shirin da yake na komawa Jam’iyyar

Duk Labarai
Rahotanni sun ce tuni, tsohon Gwamnan jihar Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya fara tetaunawa da shugaban jam'iyyar APC a shirin da yake na komawa jam'iyyar. Alamun tattaunawar tasu ta bayyana ne jiya, Alhamis, Kamar yanda Jaridar Daily Trust ta bayyana inda tace Kwankwason ya fara tattaunawa da shugaban APC, Prof. Nentawe Yilwatda Rahoton yace tuni Kwankwaso ya aikawa da hedikwatar Jam'iyyar APC da aniyarsa ta son shiga jam'iyyar a hukumance. Wata Majiya daga APC ta tabbatarwa da jaridar cewa, Kankwaso da shugaban APC din sun tattauna sosai kuma suna gab da kammala tattaunawar dan shigar Kwankwaso jam'iyyar.
Matatar man Dangote ta kori duka ma’ikatanta na Najeriya bayan da suka shiga kungiyar kwadago ta PENGASSAN

Matatar man Dangote ta kori duka ma’ikatanta na Najeriya bayan da suka shiga kungiyar kwadago ta PENGASSAN

Duk Labarai
Rahotanni sun ce matatar man fetur ta Dangote ta kori duka m'aikatanta 'yan Najeriya. Matatar tace ta yi hakanne dan canja fasalin ayyukanta. Saidai hakan na zuwane bayan da ma'aikatan suka shiga kungiyar kwadago ta ma'aikatan man fetur ta PENGASSAN. Jimullar wadanda aka kora daga aikin sun kai mutane 1000 saidai matatar bata kori ma'akatan dake mata aiki 'yan kasashen waje ba. Rikici da rashin fahimtar juna yai kamari tsakanin Dangote da kungiyar ta PENGASSAN inda ta zargi Dangoten da hana ma'aikatan matatarsa shiga kungiyar wanda tace hakan ya sabawa dokokin aiki a Najeriya. Saidai Dangote ya sha cewa shiga kungiyar kwadagon zabine ba abune na dole ba.
Kalli Bidiyon: Rahama Saidu me babban Shago inda ta mikawa namiji da yaje sayayya hannu su gaisa amma yaki yadda ya bata hannu

Kalli Bidiyon: Rahama Saidu me babban Shago inda ta mikawa namiji da yaje sayayya hannu su gaisa amma yaki yadda ya bata hannu

Duk Labarai
Rahama Saidu me babban shago ta dauki hankula inda ta mikawa daya daga cikin kwatomominta hannu su gaisa amma yaki yadda ya mika mata hannu. Inda a gefe daya kuma ta mikawa Soja Boy hannu suka gaisa. Lamarin ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa wai Namiji ne yake kin shan hannun mace amma ita tana mika masa hannu. A baya dai Soja Boy da Rahama Saidu sun gaisa hakanan ya ma rungumeta lamarin da ya jawo cece-kuce me zafi. https://www.tiktok.com/@abu_ayrin_backup/video/7553946644190989575?_t=ZS-9029A5Isqh7&_r=1
Babu kasar data kai Najeriya dadi, kada ku je ku ki dawowa, Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu shirin tafiya Jerusalem dan aikin ibada

Babu kasar data kai Najeriya dadi, kada ku je ku ki dawowa, Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu shirin tafiya Jerusalem dan aikin ibada

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gargadi kiristoci masu son tafiya jeru salem Ibada cewa kada wanda ya makale a can yaki dawowa Najeriya. Shugaban yace babu kasar data kai Najeriya 'yanci da dadi musamman idan mutum na zaune a wata kasar ba bisa ka'ida ba. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin Sakataren Gwamnatin tarayya, Sanata George Akume a yayin da kiristocin ke shirin tafiya aikin ibadar.
Karya ake min ban ce zan baiwa Yarbawa fifiko ba idan na zama shugaban kasa>>Atiku Abubakar

Karya ake min ban ce zan baiwa Yarbawa fifiko ba idan na zama shugaban kasa>>Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, ba gaskiya bane labarin da yake yawo cewa wai yace zai baiwa yarbawa kulawa da mukamai na musamman idan ya zama shugaban kasa. Atiku yace wanda ya fitar da sanarwar da yawunsa me suna Kola Johnson be sanshi ba. Atiku ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa Paul Ibe. Inda ya bukaci a yi watsi da wannan magana.