Wednesday, March 18
Shadow
In kunga dama ku ce Maula nakewa Ahmed Musa dan nace ya bani kyautar Naira Miliyan 10, ina sake nanatawa ina rokon ya bani Naira Miliyan 10>>Inji Mansurah Isah

In kunga dama ku ce Maula nakewa Ahmed Musa dan nace ya bani kyautar Naira Miliyan 10, ina sake nanatawa ina rokon ya bani Naira Miliyan 10>>Inji Mansurah Isah

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana cewa masu cewa wai Maula takewa Ahmed Musa dan tace ya bata kyautar naira Miliyan 10 hakan bai dame ta ba. Tace tana sake nanata rokonta gareshi. Sannan tace Ta samu labarin daya daga cikin matan Ahmed Musa din ta ga post dinta kuma ta yi dariya tace Allah ya cidata. A dazu Hutudole ya kawo muku Rahoton cewa, Mansurah Isah ta nemi Ahmed Musa ya bata kyautar Naira Miliyan 10.
Tun kamin Muyi aure na gayawa matata ni harkata karkar matace kuma tace min ta amince, dan haka me zaisa yanzu ta dawo tana zhaghina?>>Inji Gfresh

Tun kamin Muyi aure na gayawa matata ni harkata karkar matace kuma tace min ta amince, dan haka me zaisa yanzu ta dawo tana zhaghina?>>Inji Gfresh

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, tun kamin su yi aure ya sanar da matarsa cewa harkarsa yawanci harkar matace kuma tace ta amince. Yace amma abin takaici shine yanda a yanzu ta dawo tana zaginsa, yace kuma tana ma yi a bainar jama'a. Yace dan haka ana ta kiransa akan ya mayar da ita amma gaskiya shi ba zai iya sake zama da ita ba, yace yana mata fatan Alheri. Yace kuma ba zata taba samun miji kamarshi ba saidai idan balarabe ko Bature zata aura. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7577904598686485778?_t=ZS-91nvitC4RUH&_r=1
Tsynùwàr da El-Rufai yake yawan yiwa mutanene ta koma mai gida>>Inji Sanata Shehu Sani

Tsynùwàr da El-Rufai yake yawan yiwa mutanene ta koma mai gida>>Inji Sanata Shehu Sani

Duk Labarai
Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa a matsayin El-Rufai wanda ya taba yin gwamnan jihar Kadua, kuma ya kai shekaru 65, kamata yayi ya koma gida yana nema gafarar Allah. Yace tsinuwar da El-Rufai yake yawan yiwa mutane ce ta koma masa gida. Yace Dama idan ka yi tsinuwa idan bata hau kan wanda ka tsinemawa ba, to zata dawo kanka ne ko kan 'ya'yanka. https://twitter.com/AbbaM_Abiyos/status/1994646972071072069?t=0ymXj8-_r4vgiKSiSQ4USA&s=19
An kama Sojojin da aka sa tsaron makarantar jihar Kebbi amma suka bar makarantar har ta kai ga Tshàgyèràn Dhàjì sun je sun dàukè daliban

An kama Sojojin da aka sa tsaron makarantar jihar Kebbi amma suka bar makarantar har ta kai ga Tshàgyèràn Dhàjì sun je sun dàukè daliban

Duk Labarai
Rahotanni daga Abuja na cewa an kama sojojin da aka kai tsaron makarantar MAGA jihar Kebbi amma suka bar makarantar har ta kai ga 'yan Bindiga suka shiga suka sace dalibai 26. Daga baya dai dalibai 2 sun tsere daga hannun 'yan Bindigar wanda hakan ya sa dalibai 24 suka ci gaba da kasancewa a hannun 'yan Bindigar. An kubutar da daliban daga hannun 'yan Bindigar ba tare da sun cutu ba. Saidai an yi ta kiraye-kirayen a kama sojojin da aka kao tsaro makarantar. Wasu sojoji sun shaidawa jaridar Punchng cewa, tuni an kama sojojin da aka kai tsaro makarantar inda ake tuhumarsu kan barin makarantar wanda har ta kai ga 'yan Bindiga sun shiga sun sace daliban.
Kalli Bidiyon: Malam Abuja ba Kano bace, Wike ya gayawa Sanata Ali Ndume bayan da yacewa Wike ya daina korar Almajirai da sauran masu yawo a Abuja

Kalli Bidiyon: Malam Abuja ba Kano bace, Wike ya gayawa Sanata Ali Ndume bayan da yacewa Wike ya daina korar Almajirai da sauran masu yawo a Abuja

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sanata Ali Ndume ya ya nemi Ministan baban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike da ya daina kamawa da korar Almajirai da sauran 'yan Asalin Abuja dake yawo a tituna. Yace maimakon korarsu, kamata yayi Ministan Abujan yayi irin abinda Kano ke yi na samar da wani guri na musamman dan a rika koyawa irin wadannan mutanen sana'a. Saidai Wike yace hakan ba za yiyu ba dan Abuja ta banbanta da duk wata sauran jihar Najeriya. https://twitter.com/timmosion/status/1994327842813866034?t=I7...
Ni Bayera bene Musulmi, Kuma sai na tabbatar an fara amfani da shari’ar Musulunci a Jihohin Yarbawa saboda fiye da rabin yarbawa musulmai ne

Ni Bayera bene Musulmi, Kuma sai na tabbatar an fara amfani da shari’ar Musulunci a Jihohin Yarbawa saboda fiye da rabin yarbawa musulmai ne

Duk Labarai
Wannan bayeraben yace fiye da Rabin Yarbawa Musulmai ne dan haka sai ya tabbatar an fara amfani da shari'ar Musulunci a jihohin Yarbawa. Ya bayyana cewa, kuma nan da shekaru 20 sai ya tabbatar duka Yarbawa sun zama musulmai. https://twitter.com/Osemmuo/status/1994375784534827316?t=c1Cjr5_oDjUkM3IW8S9Atg&s=19
Kalli Bidiyon: Ana ta kiran jami’an tsaro su kama wannan malamin biyo bayan kalaman da yayi akan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Kalli Bidiyon: Ana ta kiran jami’an tsaro su kama wannan malamin biyo bayan kalaman da yayi akan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Duk Labarai
Ana ta kiraye-kirayen jami'an tsaro su kama wannan malamin saboda kalaman da yayi Biyo bayan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi. Da yawan masu kiran sun ce irin kalaman da yake yi na kamanceceniya da na masu tsaurin ra'ayin addini irin su kungiyar Bòkò Hàràm da ÌŚWÀP. Daya daga cikin masu kiran a yi bincike akan malamin shine Zagazola Makama wanda yace duk da ba'a samu wata alaqa tsakanin malamin da wata kungiyar ta'addanci ba amma ya kamata a bicikeshi. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1994470621950955632?t=V3NQKVeyqQqbV-_Elk4_Ug&s=19