Saturday, December 20
Shadow
Wannan Tauraruwar fina-finan tace Pastor Chris Okafo ya aikata Alfasha da ita, ta ji dadi, ya gamsar daita, hakan yasa ta rabu da mijinta da zummar cewa zai aureta amma yanzu gashi ta ga Hotunan aurensa da wata mata sun bayyana

Wannan Tauraruwar fina-finan tace Pastor Chris Okafo ya aikata Alfasha da ita, ta ji dadi, ya gamsar daita, hakan yasa ta rabu da mijinta da zummar cewa zai aureta amma yanzu gashi ta ga Hotunan aurensa da wata mata sun bayyana

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Kudu, Doris Ogala ta bayyana cewa,Pastor Chris Okafo ya aikata Alfasha da ita kuma ta ji dadi, ya gamsar da ita. Tace dalilin haka ma har ta rabu da mijinta bisa zummar cewa zai aureta. Tace kwatsam sai gashi taga Bidiyo da hotunan aurensa sun bayyana. Ta bayyana hakane a wani Bidiyon data wallafa a shafinta na sada zumunta inda aka ganta tana ta sharbar kuka. https://twitter.com/General_Somto/status/1999925073495441528?t=qNiwrH6bBmRRRJWv3PF-Bg&s=19
Kalli Bidiyon: Wasu Tshàgyèràn Dhàjì da aka kama sun bayyana jami’an Gwamnatin dake basu Màqàmài

Kalli Bidiyon: Wasu Tshàgyèràn Dhàjì da aka kama sun bayyana jami’an Gwamnatin dake basu Màqàmài

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kwara na cewa, an kama wasu masu garkuwa da mutane dan neman kudin fansa. Ba kamen nasu bane abin mamaki, sun kuma bayyana cewa, wani jami'in gwamnatin jihar Kwara ne ke basu makaman da suke amfani dasu. https://twitter.com/SaharaReporters/status/1999924918688100690?t=VcllUlRjc6wB1xAZ664a9w&s=19 An jima dai ana zargin wasu jami'an Gwamnati da hannu a lamarin matsalar tsaro.
Kalli Bidiyo: Duk Duniya babu Munafiqi wanda ke fadar Allah a baki amma babu shi a zuci kamar Bahaushe>>Inji Mawaki Soja Boy

Kalli Bidiyo: Duk Duniya babu Munafiqi wanda ke fadar Allah a baki amma babu shi a zuci kamar Bahaushe>>Inji Mawaki Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawaki na Arewa da yafi yin waka yana taba mata, Soja Boy ya bayyana cewa, Duk Duniya babu Munafiki kamar Bahaushe. Yace Bahaushene yafi kowa fadin Allah a baki amma babu Allahn a zuciyarsa. Ya bayyana hakane a wata hira ta musamman da aka yi dashi. https://www.tiktok.com/@agg_multimedia_services/video/7583359500980178197?_t=ZS-92C0YC12tLV&_r=1
Kalli Bidiyon: Kano da Legas ne zasu fi samun kaso me tsoka na Biliyan 100 dan tallafawa harkar Ilimi>>Inji Dangote

Kalli Bidiyon: Kano da Legas ne zasu fi samun kaso me tsoka na Biliyan 100 dan tallafawa harkar Ilimi>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, Kano da Legas ne zasu fi amfana da Naira Biliyan 100 da ya ware na tallafawa harkar Ilimi. Yace dalili shine wadannan jihohi sun fi sauran Jihohin Najeriya yawan Al'umma. Yace zasu raba kudadenne zuwa kowacw karamar hukuma kuma zasu tabbatar kowace Karamar hukuma ta samu kudin daidai wadaida. https://twitter.com/thecableng/status/1999872796328157682?t=MKulHbPi-MWstwyE4IZsyQ&s=19
An yi min Wahayi Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba, Sannan wani matashine dan kimanin shekaru 37 zai zama shugaban kasa ya kayar da Tinubu zabe>>Inji Wannan faston

An yi min Wahayi Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba, Sannan wani matashine dan kimanin shekaru 37 zai zama shugaban kasa ya kayar da Tinubu zabe>>Inji Wannan faston

Duk Labarai
Wannan wani Fasto ne da ya bayyana cewa, An masa wahayin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba. Yace wani sabon matashi dan kimanin shekaru 37 ne zai fito ya co zabe. Yace matashin zai kawai da duk tsaffin 'yan siyasar kasarnan ya kawo canji da zaiwa kowa dadi. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1999528174519030160?t=24qf0qO5nSB_U7-j4KcLzg&s=19
Da Duminsa: Kasar Burkina Faso taqi sàkò sojojin Najeriya 11 data kama, Tàcè bata yadda kuskurene yasa suka shiga sararin samaniyarta ba da izini ba

Da Duminsa: Kasar Burkina Faso taqi sàkò sojojin Najeriya 11 data kama, Tàcè bata yadda kuskurene yasa suka shiga sararin samaniyarta ba da izini ba

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Burkina Faso sun bayyana cewa, kasar ta ki yadda ta sako sojojin Najeriya 11 data kama da jirginsu C-130. Rahoton yace kasar ta Burkina Faso ta dauke sojojin daga inda ta ajiyesu a baya inda a yanzu ta kaisu wani waje me matsanancin tsaro. Kasar ta Burkina Faso ta yi imanin cewa sojojin na daga cikin wanda suka hana juyin Mulki a kasar Benin Republic. Dan Jarida, Oseni Rufai ya bayyana cewa ya samu daga majiya me karfi cewa har zuwa yanzu Hukumomin Najeriya basu tuntubi kasar Burkina Faso kan sakin sojojin ba. Najeriya dai tace sojojin na kan hanyar zuwa kasar Portugal ne jirgin su ya samu tangarda suka sauka a Burkina Faso.
Ana rade-radin, Janar Christopher Musa ka iya maye Kashim Shettima a matsayin mataimaki Shugaba Tinubu a 2027

Ana rade-radin, Janar Christopher Musa ka iya maye Kashim Shettima a matsayin mataimaki Shugaba Tinubu a 2027

Duk Labarai
Rahotanni na yawo cewa, Sabon Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ka iya maye gurbin mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima a matsayin mataimakin shugaban kasa a 2027 Wani me sharhi akan al'amuran yau da kullun ne na siyasar Najeriya ya bayyana hakan inda yace ya samu wannan labari ne daga wata majiya me karfi. https://twitter.com/ChinonsoCharl15/status/1999487323214610651?t=nx502zWrcwwmSnrHHNOx5A&s=19
Da Duminsa:Shugaba Tinubu ya amince a sake Bude Depot (Makarantar Horas da sojoji) a Abakaliki

Da Duminsa:Shugaba Tinubu ya amince a sake Bude Depot (Makarantar Horas da sojoji) a Abakaliki

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince a sake bude wata Depot watau makarantar horas da sojoji a Bakaliki dake jihar Ebonyi. Shugaban sojojin Najeriya, Lt. General Waidi Shuaibu ne ya bayyana haka a Zaria wajan yaye sabbin kurtan sojoji guda 3,439 da aka yi ranar Asabar. Yace wannan bude sabon depot zai baiwa sojojin damar daukar karin sojoji da zasu samar da tsari a Fadin Najeriya. Zuwa yanzu kenan yawan Depot din horas da sojoji da ake dasu a fadin Najeriya sun kai 3. Kaduna ⁠Osogbo ⁠Abakaliki