Friday, January 2
Shadow
Hukumar Sojojin Najeriya ta bukaci mutanen Sokoto su dawo da baraguzan BòmàBòmàn da kasar Amurka ta jefa

Hukumar Sojojin Najeriya ta bukaci mutanen Sokoto su dawo da baraguzan BòmàBòmàn da kasar Amurka ta jefa

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta bukaci mutanen jihar Sokoto da su dawo da baraguzan bama-bamai wanda kasar Amurka ta Jefa. Rahotanni sun ce wasu 'yan gwangwan sun kwashe baraguzan bama-baman da Amurka ta jefa a jihar. Saidai hukumar sojojin Najeriya tace mutane su dawo da wannan baraguzan Bama-baman dan akwai ma wanda basu tashi ba dan kada su cutar da mutane. Hukumar sojojin ta nemi hakanne ta bakin kakakin hukumar a yayin da yake ganawa da manema labarai. https://twitter.com/i/status/2007010725420741018
Bamu so Abinda ya faru tsakanin Kwankwaso da Ganduje ya faru da Abba>>Inji Tijjani Gandu

Bamu so Abinda ya faru tsakanin Kwankwaso da Ganduje ya faru da Abba>>Inji Tijjani Gandu

Duk Labarai
Daya daga cikin mawakan Kwankwasiyya, Tijjani Gandu ya fito ya bayyana cewa basa son Rabuwar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da Shugaban Tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso. Ya bayyana cewa ba wai basa son Abba ya bar NNPP bane. Amma abinda suke cewa, shine Duk inda Abba zai tafi, su tafi tare da Kwankwaso. Hakan na zuwane bayan da rade-radi suka yi yawa cewa, Abba zai koma jam'iyyar APC. Rade-radin sun kara karfi bayan da aka ga Abba ya gana da shuwagabannin jam'iyyar APC na Kano.
Kalli Bidiyon: Matashi wanda yayi ikirarin shi dan dariqa ne ya dauki hankula bayan da aka ganshi yana shan Qiya

Kalli Bidiyon: Matashi wanda yayi ikirarin shi dan dariqa ne ya dauki hankula bayan da aka ganshi yana shan Qiya

Duk Labarai
Matashi wanda yayi ikirarin cewa shi dan darikar Tijjaniyya ne ya dauki hankuka bayan da aka ganshi yana shan giya. Matasashin yace duk wanda baya darikar Tijjaniyya an barshi abaya. A cewarsa a Darikar Tijjaniyya ce kadai mutum zai sha Giya. https://www.tiktok.com/@anas_n_f_s/video/7589927983427685644?_t=ZS-92iE2ijlUTx&_r=1
Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya ce ya yafewa Sanata Natasha Akpoti abinda ta masa. Sannan yace ya baiwa lauyoyin sa umarnin su janye karar da ya shigar akanta dama duka wasu da ya ke kararsu akan sun bata masa suna. Yace dalilinsa na yin haka shine Faston sa ya masa wa'azi kuma wa'azin ya shigeshi. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2006714564621037783?t=d8iGOafoZPdJz0fJ7bzYbw&s=19