Wednesday, September 16
Shadow
Tacw bata damu ta shiga Jahannama ba saboda auren Kirista

Tacw bata damu ta shiga Jahannama ba saboda auren Kirista

Duk Labarai
Wannan wata matashiyace me suna Mira data bayyana cewa a matsayinta na musulma ta auri Kirista. Tace kuma masu ce mata wai zata shiga wuta to a shirye take ta shiga Jahannama indai akan auren Kirista ne. Har ma ta hada Editin inda ta nuna kanta a Jahannama. Saidai da yawa na ce mata hakan Izgili ne ga Allah. https://www.tiktok.com/@thaarealprincess_/video/7684571462681775380?_r=1&_t=ZN-99iaymsPQTG
Mutane 3 sun shigar da Peter Obi kara a kotu kan takardun makarantarsa

Mutane 3 sun shigar da Peter Obi kara a kotu kan takardun makarantarsa

Duk Labarai
Jigo a jam'iyyar Labour Party, Mr. Abayomi Arabambi ya shigar da kara a gaban kotu inda yake neman WAEC da jami'ar UNN, da Hukumar bautar kasa ta NYSC su bayyana ainahin takardun karatun dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi Yace ya aikawa Hukumomin da bukatar hakan amma sun ki, dan haka yake neman kotu ta tursasasu. Bayanshi, akwai kuma mutane 2 da suma suka shigar da kara akan neman takardun ainahi na karatun Peter Obi wanda jimullarsu ya kai 3 kenan. Arabambi yace bawai yana zargin takardun bogine Peter Obi ke amfani dasu ba, yana son wadannan hukumomi su bayyanawa Duniya ainahin takardun karatun na peter Obine.
Kalli Bidiyon: Yanda Inyamurai ke cewa Gwamnan jiharsu ta Imo ya dauki mataki kan Musulmai saboda sun gansu suna sallah ranar Juma’a akan Titi

Kalli Bidiyon: Yanda Inyamurai ke cewa Gwamnan jiharsu ta Imo ya dauki mataki kan Musulmai saboda sun gansu suna sallah ranar Juma’a akan Titi

Duk Labarai
Ganin Musulmai suna sallah akan Titi a jihar Imo ya jawo cece-kuce a wajan Inyamurai na jihar inda suke kira ga gwamnan jihar da ya dauki mataki kan Musulman. Bidiyon lamarin ya watsu a kafafen sadarwa inda iyamuran ke ta suka suna fadar kalaman da basu dace ba. https://twitter.com/BiaPulse/status/2098845012574499301
Ba zamu dawo da tallafin man fetur ba>>Inji Gwamnatin Tarayya

Ba zamu dawo da tallafin man fetur ba>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa ba zata dawo da biyan Tallafin man fetur ba. Gwamnatin ta bayyana hakane ta bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga. Bayo yace suna sane da kiraye-kirayen da ake game da cire tallafin man fetur da kuma maganar da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar yayi na cewa zai dawo da tallafin man fetur. Yace amma duk da wannan matsi ba zasu dawo da tallafin man fetur din ba. Dalili shine idan aka dawo da biyan tallafin man fetur din, ci gaban da aka samu a gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zasu ruguje.