Thursday, February 26
Shadow
Hankalin ‘yan Kudu ya tashi sosai suna fadar ashe satar mai zai kawo ku? Bayan da aka bayyana Jihar Rivers a matsayin inda sojojin Amurka zasu sauka idan sun zo Najeriya

Hankalin ‘yan Kudu ya tashi sosai suna fadar ashe satar mai zai kawo ku? Bayan da aka bayyana Jihar Rivers a matsayin inda sojojin Amurka zasu sauka idan sun zo Najeriya

Duk Labarai
Wani bature me suna Dr. Walid Phares ya bayyana cewa, yana bayar da shawara ga shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya girke sojojin kasar Amurka a Birnin Fatakwal na Jihar Rivers inda yace ta nan ne za'a rika samun damar kai kayan agaji daga Choci-Choci na Duniya. Saidai wannan magana batawa 'yab kudu da yawa dadi ba musamman ma 'yan Jihar ta Rivers inda suke cewa ba yakar matsalar tsaro zata kawo Amurka Najeriya ba, Satar mai ne zai kawo su. Shugaban kasar Amurka, Donald Trump dai ya bayyana aniyarsa ta son Afkawa Najeriya da hare-hare da sunan yaki da masu yiwa kiristoci Khisan Kyiyashi.
Wani Bature me fada a ji yayi kira ga Trump ya tabbatar da Kafuwar kasar Biafra

Wani Bature me fada a ji yayi kira ga Trump ya tabbatar da Kafuwar kasar Biafra

Duk Labarai
A yayin da ake tsaka da tattauna barazanar shugaban kasar Amurka Donald Trump ta kawo hari Najeriya da sunan cewa zai baiwa kiristoci kariya daga Khisan Khiyashi da ake musu. Wakili a kungiyar tsaron kasashen Turawa ta NATO me suna Gunther Fehlinger yayi kira ga Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya tabbatar da kafuwar kasar Biafra. https://twitter.com/GunterFehlinger/status/1985252165066092817?s=19 Hakan yasa masu sharhi da yawa ke bayyana cewa, dama abinda ya tado da maganar cewa ana yiwa Koristoci khisan Kyashi kenan ana son kafa kasar Biafra ne.
Hattara: Wallahi Duk sojhan America da ya Shyigho Najeriya saidai Bhuzunsa>>Inji Mawakin Najeriya, Portable

Hattara: Wallahi Duk sojhan America da ya Shyigho Najeriya saidai Bhuzunsa>>Inji Mawakin Najeriya, Portable

Duk Labarai
Mawakin Kudu, Portable ya gargadi sojojin America da cewa kada su shigo Najeriya. Portable ya bayyana cewa, Duk sojan America da yayi gigin Shigowa Najeriya ba lallai ya koma gida ba. Ya bayyana hakane a wata hira da suka yi da wani sojan kasar Amurka dan Asalin Najeriya. Portable yace me yasa sojan bai tsaya yawa kasarsa yaki ba? https://twitter.com/dammiedammie35/status/1985239424485998913?t=t7U0UGlFtrzxGgQwzPHudw&s=19
Kar kowa ya tayar da hankalinsa, Ku bar Trump ya aiko sojojin Amurka Najeriya, Ni kadai gayyane na ishesu>>Inji Mujahid Asari Dokubo

Kar kowa ya tayar da hankalinsa, Ku bar Trump ya aiko sojojin Amurka Najeriya, Ni kadai gayyane na ishesu>>Inji Mujahid Asari Dokubo

Duk Labarai
Tsohon shugaban tsageran Naija Delta, Mujahiddeen Asari Dokubo Ya bayyana cewa a bar sojojin Amurka su shigo Najeriya, shi kadai ya ishesu. Ya bayyana cewa Kasar Amurka kasar Mahaukatace shiyasa suka zabi Mahaukaci a matsayin Shugaban kasa. Asari Dokubo ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta inda aka jishi yana cewa a barsu su zo. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1985231684393116001?t=lh0TI6DrWD0iP-qAc4xZGg&s=19
Mu a yankin Inyamurai da kaso 95 cikin 100 Kiristoci ne, ‘yan uwan mu Kiristoci ne ke shekye mutanen mu>>Inji Gwamnan Anambra, Charles Soludo

Mu a yankin Inyamurai da kaso 95 cikin 100 Kiristoci ne, ‘yan uwan mu Kiristoci ne ke shekye mutanen mu>>Inji Gwamnan Anambra, Charles Soludo

Duk Labarai
Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya bayyana cewa, a yankinsa na kudu maso gabas na Inyamurai wadanda kaso 95 cikin 100 Kiristoci ne, masu Khashye mutanensu kiristoci ne. Ya bayyana hakane a wajan wani taro da aka gudanar Ranar Lahadi inda yake martani kan zargin Khisan Khiyashi da aka ce anawa kiristoci a Najeriya. Ya bayyana cewa dan haka maganar ta wuce ta addini. Yace kuma Gwamnatin Najeriya na iya bakin kokarinta wajan shawo kan matsalar tsaron. Sannan ya bayyana fatan nan gaba kasar zata magance wannan matsala ba tare da wani haufi ba.
Rahoto: Mutane Dubu arba’in da bakwai ne aka shekye a kasar Amurka a shekarar 2024 saboda rhikiche-rhikichen Bhìndhìghà

Rahoto: Mutane Dubu arba’in da bakwai ne aka shekye a kasar Amurka a shekarar 2024 saboda rhikiche-rhikichen Bhìndhìghà

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Mutane 47,000 ne aka Shekye a kasar Amurka saboda rikicin Bindiga a shekarar 2024 data gabata. Kasar Amurka na fama da rikicin mutane da a wasu lokutan kawai suke daukar Bindiga su shiga wajan taron mutane su bude musu wuta. Hakan ya faru da shugaban kasar Amurkar, Donald Trump inda aka kai masa hari na yunkurin Khisa amma ya tsallake rijiya da baya. A irin wannan yanayi ne Trump din ke cewa wai zai kawowa Najeriya dauki a yayin da kasarsa na fama da matsalar hare-haren.
Kalli Hoto: Koristoci Masu tunanin Shugaban kasar Amurka Donald Trump zai zo ya basu kariya, ku kalli Wannan hoton, shima Trump din a cikin gilashi wanda harshashi baya iya hudashi yake magana a wajan taro a cikin kasarsa saboda tsoro

Kalli Hoto: Koristoci Masu tunanin Shugaban kasar Amurka Donald Trump zai zo ya basu kariya, ku kalli Wannan hoton, shima Trump din a cikin gilashi wanda harshashi baya iya hudashi yake magana a wajan taro a cikin kasarsa saboda tsoro

Duk Labarai
Wani me suna Osazenoo ya bayyana cewa, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump a cikin gilashi yake magana a wajan taro saboda tsoron kada wani ya bindigeshi. Yace amma wai wannan mutuminne wasu a Najeriya suke tunanin zai zo ya basu kariya? https://twitter.com/osazenoo/status/1985131176919482735?t=L4PAxGWeWbMWUYhuZKbAuA&s=19 Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa, zai kawowa Kiristoci wadanda yace anawa Khisan kiyashi a Najeriya dauki.
Ban san me yasa Kasashen da ke da Arzikin man Fetur ne kadai Shugaban kasar mu yake son Yin Yhaqi dasu ba>>Baturen Amurka ya bayyana mamakinsa

Ban san me yasa Kasashen da ke da Arzikin man Fetur ne kadai Shugaban kasar mu yake son Yin Yhaqi dasu ba>>Baturen Amurka ya bayyana mamakinsa

Duk Labarai
Baturen Amurka, Spencer Hakimian ya bayyana cewa, abin mamaki ne yanda Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, Kasashen dake da Arzikin man fetur ne kadai yake son yin yaki dasu. Ya kawo misalin kasashen da Trump din yake son yin yaki dasu irin su, Iran, Venezuela da Najeriya. A karshe yace akwai alamar wata makarkashiya a lamarin. https://twitter.com/SpencerHakimian/status/1984741183839494266?t=TwAvd4-gN9_dcHswTVusoA&s=19
Da Duminsa: A karo na biyu, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump yace ba fa zai ci gaba da ganin cin kashin da akewa Kiristoci a Najeriya ba sai ya kawo musu dauki

Da Duminsa: A karo na biyu, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump yace ba fa zai ci gaba da ganin cin kashin da akewa Kiristoci a Najeriya ba sai ya kawo musu dauki

Duk Labarai
Donald Trump ya jaddada cewa Amurka za ta iya tura dakaru Najeriya ko kuma kaddamar da hare-hare domin hana abin ya kira kisan Kiristoci da ake yi. Ya shaida wa manema labarai cewa ba zai bari a ci gaba da kisan ba. "Ana kashe kiristoci da dama a Najeriya kuma adadi da yawa, ba zan bari a ci gaba ba." in ji Trump. Fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da samun hadin kan Amurka wajen yaƙi da mayaka masu tsattsaran ra'ayin addini tare da musanta cewa mayakan sun fi kashe kiristoci. A watan da ya gabata Amurka ta saka Najeriya cikin jerin kasashen da take da damuwa da su kan take ƴancin addini. A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Asabar, Mista Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji don kakkaɓe abin da ya kira ƴanta'adda mas...
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara kasar Amurka ranar Talata dan shawo kan kasar karta Afkawa Najeriya da Khare-Khare

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara kasar Amurka ranar Talata dan shawo kan kasar karta Afkawa Najeriya da Khare-Khare

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara kasar Amurka dan jawo hankalin kasar da fahimtar da ita halin da ake ciki a Najeriya ba kamar yanda ake cewa ana yiwa Kiristoci Khisan Khiyashi ba. Rahoton yace Shugaban kasar Amurkar ya wakilta mataimakinsa, JD Vance ya gana da shugaba Tinubu a yayin ziyarar. Kafar Sahara Reporters ce ta bayyana haka inda tace ta samu bayanan ne daga fadar shugaban kasa Bola Tinubu. Hakan na zuwane a yayin da ake tsaka da fargabar kawo hari na kasar Amurka a Najeriya.