Sunday, March 1
Shadow
Da Duminsa: Jami’ar da aka ce ta baiwa Rarara Digirin girmamawa tace damfarar Mawakin aka yi, bata san da maganar ba

Da Duminsa: Jami’ar da aka ce ta baiwa Rarara Digirin girmamawa tace damfarar Mawakin aka yi, bata san da maganar ba

Duk Labarai
Rahotanni sun ce jami'ar The European-American University da aka ce ta baiwa Dauda Kahutu Rarara Digirin girmamawa na Dr. Tace bata san da maganar ba. Jami'ar tace wadanda suka ce su wakilanta ne har suka baiwa Dauda Kahutu Rarara Digirin karya suke ba wakilanta bane. Kafar Daily Nigerian ta ruwaito cewa, a sanarwar da jami'ar ta fitar tace zata kai wadanda sukawa Rarara wannan Damfara kotu dan a hukuntasu.
Kalli Yanda matan da ake zargin an baiwa kudi dan su fito tarbar shugaba Tinubu a Kaduna ke kulle fuskokinsu basu son kyamara ta daukesu hoto

Kalli Yanda matan da ake zargin an baiwa kudi dan su fito tarbar shugaba Tinubu a Kaduna ke kulle fuskokinsu basu son kyamara ta daukesu hoto

Duk Labarai
Wadannan wasu matane da ake zargin an baiwa kudi dan su fito su tarbi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a Kaduna. Saidai sun ki yadda kyamara ta dauki fuskokinsu inda suke kulle fuskokin. Tsohuwar hadimar Shagaban kasa, Lauretta Onochie ce ta wallafa hoton inda tace an tursasa matan ne su yi tallar Tinubu. https://twitter.com/Laurestar/status/1969359202163261601?t=8t3C8PF-UvpUXRXcCRglAw&s=19
Kalli Bidiyo: Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Gayu ta zama ta farko a masana’antar data mallaki wayar iPhone 17 Pro ta sama da Naira Miliyan 2

Kalli Bidiyo: Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Gayu ta zama ta farko a masana’antar data mallaki wayar iPhone 17 Pro ta sama da Naira Miliyan 2

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Gayu ta kasance jaruma ta farko a masana'antar da ta fara bayyana sayen sabuwar wayar iPhone 17 pro. Wayar dai wadda kamfanin Apple ya sanar da fitowarta a makon da ya gabata itace ake ta magana a gari musamman tsakanin masoya wayoyi. Farashin wayar ya haura Naira Miliyan 2 inda a wani gurin ma ana samunta akan Naira 2,990,000. An ga Jaruma Ummi Gayu a wani Bidiyo da ya watsu sosai tana nuna wayar a hannunta. https://www.tiktok.com/@yar.fulani.yola/video/7551857713538403605?_t=ZS-8zsbi5ZEU7t&_r=1
Mutanen Kaduna sun ki fitowa su tarbi Tinubu shine suka samo yara ‘yan makaranta suka zuba akan Titi>>Inji Tsohuwar Hadimar Shagaban kasa, Lauretta Onochie

Mutanen Kaduna sun ki fitowa su tarbi Tinubu shine suka samo yara ‘yan makaranta suka zuba akan Titi>>Inji Tsohuwar Hadimar Shagaban kasa, Lauretta Onochie

Duk Labarai
Tsohuwar hadimar shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Lauretta Onochie ta bayyana cewa, ziyarar da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai jihar Kaduna bata yi Armashi ba. Ta godewa mutanen Kaduna saboda kin fitowa su tarbi shugaban kasar inda tace sai yara aka samo aka zuba akan titi. Ta bayyana hakane a shafinta na X. Ta kara da cewa, wannan sakamakon mulki da rashin bin doka kenan. https://twitter.com/Laurestar/status/1969161660553187344?t=S78sFGCVGhA-gpmwqQO5iA&s=19