Usman da Umar (AS) zasu iya canja hukuncin da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi kuma hakan yayi daidai>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi
Babba Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, Sahabban Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Umar da Usman (AS) zasu iya canja hukuncin sa Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) yayi kuma hakan yayi daidai.
Yace Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya basu wannan matsayi na cewa, duk hukuncin da suka yi ya zama shari'a.
Malam ya bayyana hakane a wajan karatun da yake ranar Juma'a a masallacin Sultan Bello dake Kaduna a ranar 22/8/2025.
Wakilin hutudole ya halarci wajan karatun inda malam yayi wannan maganane a yayin da yake bayar da misalin ikirarin 'yan shi'a na cewa, Khalifanci Aliyu (AS) ne ya kamata a baiwa kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya bar wasiyya kan hakan.
Malam yace ko da ace Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya bar wasiyya akan hakan am...







