Tuesday, December 16
Shadow
An kama wasu ‘yan kasar China 14 a Najeriya bisa aikata miyagin Laifuka za’a mayar dasu kasarsu, Ji laifukan dansuka aikata

An kama wasu ‘yan kasar China 14 a Najeriya bisa aikata miyagin Laifuka za’a mayar dasu kasarsu, Ji laifukan dansuka aikata

Duk Labarai
Babbar kotun tarayya dake da zama a Ikoyi jihar Legas ta daure wasu 'yan kasar China 14 da aka kama bisa zargin aikata damfarar yanar gizo da taimakawa 'yan ta'adda. Hukumar EFCC tace ta kama su ne a wani samame data kai a cikin birnin legas din a watan December 19, 2024. EFCC tace 'yan Chinar na daga cikin mutane 792 data kama kuma an gurfanar dasu a gaban mai shari'a Justice Daniel Osiagor. Da farko sun ki amsa laifukan nasu amma daga baya sun amsa cewa sun aikata laifukan. Lauyoyin EFCC, T.J. Banjo da M.S. Owede sun nemi kotu ta daure wadanda ake zargin kuma lauyoyin wadanda ake zargin basu nemi kada a yi hakan ba. A karshe an yanke musu hukuncin daurin shekara daya a gidan yari ko kuma biyan tarar Naira miliyan daya sannan da zarar sun gama zaman gidan yarin ko biyan ta...
Yanda ‘yansanda suka min fàdè a bakin boda>>Wata ‘yar Najeriya data je cirani kasar Libya ta dawo da kyar ta bayar da labari

Yanda ‘yansanda suka min fàdè a bakin boda>>Wata ‘yar Najeriya data je cirani kasar Libya ta dawo da kyar ta bayar da labari

Duk Labarai
Wata 'yar Najeriya data je Cirani kasar Libya ta dawo da kyar ta bayar da labarin irin wahalar data sha. Matar sunanta Olaonipekun Adenike kuma shekarunta 30 tana da 'ya'ya 2. Tace ita kadai ce a wajen mahaifiyarta dan duk 'yan uwanta sun mutu. Tace ta so yin karatu har ta fara amma rashin kudi yasa dole ta hakura. Tace ta hadu da wata kawar mahaifiyarta a facebook wadda take zaune a kasar Libya wadda ta tambayeta abinda take yi inda ta zayyana mata komai, tace daga nan ne sai kawai magaifiyartata tace mata zata taimaketa musamman saboda irin kirkin da mahaifiyarta ta mata lokacin suna tare. Tace ta shirya ta je Libya aikatau. Tace ta ji dadin hakan inda suka tashi daga garinsu, Sagamu dake jihar Ogun suka tafi Libya. Tace sun je Legas suka je Kano suka shiga Nijar, tace ...
Kalli yanda uwa ke zane diyarta saboda diyar tawa uwar kwacen saurayi

Kalli yanda uwa ke zane diyarta saboda diyar tawa uwar kwacen saurayi

Duk Labarai
Fada saboda saurayi ya zama ruwan dare musamman tsakanin dalibai 'yan mata a makarantun jami'a. Ko da a farkon watannan na Yuni da muke ciki, sai da aka ga wani Bidiyo yanda aka ci zarafin wata budurwa, 'yan mata da yawa suka taru akanta suna duka saboda saurayi. Abin takaici shine yanda aka dauki Bidiyon faruwar lamarin aka watsa shi a kafafen sada zumunta kowa yaga irin abinda akawa budurwar. Lamarin ya farune a jihar Ogun, kuma kawayen budurwar sun bayyana cewa da sanin mahaifiyarsu suka aikata wannan danyen aiki dan haka basa shakkar wani ya gani. Tuni dai hukumar 'yansandan jihar ta sanar da fara binciken kan lamarin. Saidai ko da an hukunta wadanda sukawa wannan Budurwa wannan cin zarafi, ba za'a iya goge tozarcin da suka mata ba. Uwa na dukan 'yarta saboda zata ma...
Bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn

Bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn. An tattaro bayanan yawan bashin da ake bin Najeriya har zuwa watan March 31, 2025 inda daga nan ne aka samu wadannan bayanai. A shekarar data gabata, 2024 dai yawan bashin da ake bin Najeriya Naira Tiriliyan N121.67tn ne wanda hakan ke nufin a yanzu bashin ya karu da Naira Tiriliyan N27.72tn ko ace da kaso 22.8 cikin 100. Ofishin dake kula da bashin da Najeriya ke ciyowa DMO ne ya fitar da wadannan bayanai ranar Juma'a. Yawan bashin da ake bin Najeriya na karuwa ne saboda kara cin bashin da gwamnatin tarayya take da kuma faduwar darajar Naira da sauransu. Gwamnatin tarayyar Najeriya dai na dogaro da bashi dan gudanar da ayyukanta, kuma tana cin bashin ne daga cikin gida Najeriya d...
Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa sabon daftarin doka hannu wanda ya baiwa jihohin Najeriya damar samarwa da rarraba wutar Lantarki a jihohinsu. Tun a shekarar 2024 daftarin dokar ya wuce amincewar 'yan majalisa inda ake jiran shugaba Tinubu ya saka hannu amma bai saka ba sai a yau. Masana sun ce hakan ya canja kula da wutar lantarki a Najeriya wanda a baya yake hannun Gwamnatin tarayya, a yanzu jihohi ne zasu rika samar da wutar. Hakanan ana tsammanin wannan sabuwar dokar zata jawo masu zuba jari a harkar sannan zata karfafa gasa tsakanin jihohin wanda hakan zai inganta samar da wutar Lantarkin.
Ji sabon mukamin da Shugaba shugaba Tinubu ya baiwa Ganduje bayan sauka daga shugaban APC

Ji sabon mukamin da Shugaba shugaba Tinubu ya baiwa Ganduje bayan sauka daga shugaban APC

Duk Labarai
Rahotanni sun ce shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shirin baiwa tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje sabon mukami. Hakan na zuwane kwana daya da saukat Ganduje daga mukamin shugaban jam'iyyar APC. Wata majiya ta bayyanawa jaridar Vanguard cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu kwanannan zai bayyana Ganduje a matsayin jakadan Najeriya zuwa kasar waje. A kwanakin baya dama an yada rade-radin cewa, Shugaba Tinubu na shirin baiwa Ganduje mukamin jakadanci amma maganar ta lafa. Wasu majiyoyi sun ce Ganduje a wancan lokacin ya ki karbar mukamin jakadane saboda yana jan zarensa a matsayin shugaban jam'iyyar APC wanda yana ganin kujerar shugaban jam'iyya tafi karfin ta Jakada. Da yawa a wancan lokaci sun yi mamakin irin karfin da Ganduje ke dashi a gwamnatin Tinubu ...
Mun yi babban rashi>>Shugaba Tinubu ya gayawa yi jimamin rasuwar Dantata

Mun yi babban rashi>>Shugaba Tinubu ya gayawa yi jimamin rasuwar Dantata

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi jimamin rasuwar Aminu Dogo Dantata a sakon da ya fitar ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga. Shugaban yace wannan rashi ne da Najeriya ta yi baki daya. Yace za'a tuna Dantata da kasuwancin da yayi da kuma taimakawa da yayi wajan hadin kan Najeriya ta wajan bayar da tallafin da ya amfani mutane da yawa. Tinubu ya bayyana Dantata a matsayin mutumin da ya bashi gudummawa wajan shawara me kyau. A karshe ya mikawa iyalan mamacin sakon ta'aziyya.
Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaban APC na riƙo

Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaban APC na riƙo

Duk Labarai
Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam'iyyar na riƙo. Wannan na zuwa ne bayan tsohon gwamnan na jihar Kano ya ajiye muƙamin a ranar Juma'a, sannan aka naɗa Dokta Ali Bukar Dalori a matsayin wanda zai riƙe muƙamin, kafin a kai ga zaɓen wanda zai maye gurbinsa. Mutane dai sun yi zargin ruwa ba ya tsami banza, ko kuma dai da walakin goro a miya amma uwar jam'iyyar ta yi watsi da wannan hasashe. Bala Ibrahim shi ne daraktan yaɗa labarai na jam'iyyar ta APC, ya ce "Game da batun wanda zai maye gurbin shugaban jam'iyyar da sauka, dama jam'iyya na da kundin tsarin mulki wanda ya yi tanadi irin wannan wanda idan shugaban jam'iyya ya sauka daga muƙaminsa to za a zaɓi ɗaya daga cikin mataimakansa biyu...