Friday, December 5
Shadow
Ba gaskiya bane cewa Sojoji dubu goma sun tsere daga aiki>>Inji Hukumar sojojin Najeriya

Ba gaskiya bane cewa Sojoji dubu goma sun tsere daga aiki>>Inji Hukumar sojojin Najeriya

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta karyata cewa, Sojoji dubu goma sun tsere daga aiki. Wasu rahotanni a kafafen sada zumunta sun bayyana cewa, Saboda sojoji dubu 10 sun tsere daga aikin soja duk wanda ya kai sama da shekaru 18 dole zai shiga aikin soja. Saidai hukumar sojojin sun bayyana cewa wannan labarin karya ne. A baya dai Hukumar sojojin ta sanar da daukar sabbin sojoji 24,000. https://twitter.com/HQNigerianArmy/status/1991787697976000989?t=xPFnCke9fTejeYkzVK3vdQ&s=19
A jihar Ogun ma ana zargin Tshàgyèràn dhaji sun je sun dauki Mùtànè

A jihar Ogun ma ana zargin Tshàgyèràn dhaji sun je sun dauki Mùtànè

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Ogun sun bayyana cewa ana zargin fulani da kai hari wani gurin da 'yan kasar China ke aiki inda suka yi garkuwa da 'yan kasar Chinan su 2. Daya daga cikin wadanda ke aiki da dan Chinan ne ya bayyana hakan i da yace Fulani ne suka je suka dauke shugabansu. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1992114335746007064?t=Xv4Z7Yu5DXjGHxjDKuSx2A&s=19 https://twitter.com/omoelerinjare/status/1991996785901113706?t=9_w3v3wpd9MNX7oPx0c65w&s=19 Lamarin a karade kafafen sada zumunta inda Rahotanni suka ce ya farune ranar Juma'a da yamma.
Kalli Bidiyon: Allah Sarki Matar Gfresh, Maryam na ta banbami bayan ganin shi sunata rùngùmèRùngùmè shi da tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna

Kalli Bidiyon: Allah Sarki Matar Gfresh, Maryam na ta banbami bayan ganin shi sunata rùngùmèRùngùmè shi da tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna

Duk Labarai
Maryam matar Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ta bayyana fushinta game da ganin Yanda Gfresh da tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna ke rugumerungumen juna. A wata Murya dake ta yawo a kafafen sada zumunta, an ji Maryam na cewa, kotu ce zata rabasu sannan kuma tace zata je ta ajiye masa dansa, Khalid. https://www.tiktok.com/@nuciescollection2/video/7575243635348868359?_t=ZS-91b1JFOupLE&_r=1 Hakanan a wani Bidiyo data wallafa a shafinta na Tiktok an ga Maryam na cewa Allah ya kawo mata dauki. https://www.tiktok.com/@maryamnikicminaj/video/7575057516871142676?_t=ZS-91b0naPe2C1&_r=1
Da Duminsa:Labaran da muke samu sun tabbatar mana muna daf da inda ake rike da daliban Kebbi>>Inji Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle

Da Duminsa:Labaran da muke samu sun tabbatar mana muna daf da inda ake rike da daliban Kebbi>>Inji Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle da a yanzu haka ke jihar Kebbi ya bayyana cewa bayanan sirri da suke samu sun tabbatar musu da cewa suna daf da inda daliban da aka sace suke. Yace sun baza jami'an tsaro a duk wata hanya da za'a iya bi dan guduwa da daliban. Sannan ya bayar da yakinin cewa nan ba da jimawa ba za'a kubutar da daliban. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1991986856465244651?t=oiEqSYq2kCEWkdwODzyHLw&s=19
Kada Ku tayar da hankulanku ni dinnan an taba yanke min hukuncin daurin rai da rai tare da Obasanjo amma gashi mun samu ‘yanci>>Shehu Sani ya gayawa Inyamurai kan yankewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai

Kada Ku tayar da hankulanku ni dinnan an taba yanke min hukuncin daurin rai da rai tare da Obasanjo amma gashi mun samu ‘yanci>>Shehu Sani ya gayawa Inyamurai kan yankewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai

Duk Labarai
Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya baiwa Inyamurai baki kan hukuncin daurin rai da rai da akawa Nnamdi Kanu. Shehu Sani yace ba karshen rayuwa bane. Yace shi da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo an taba musu daurin rai da rai amma gashi har sun kammala sun samu 'yanci. Ya bayyana hakane a shafinsa na X. https://twitter.com/ShehuSani/status/1991945260973400549?t=7_6BBMEhsOur3K7IGlYMlQ&s=19
Kwalayen Indomie dana sàtà ‘yan matana 3 na rabawa amma da aka kamani cikinsu babu wadda ta kawo min ziyara a gida  yari>>Inji Barawon Indomie da aka yankewa hukuncin daurin shekaru 2 a gidan yari

Kwalayen Indomie dana sàtà ‘yan matana 3 na rabawa amma da aka kamani cikinsu babu wadda ta kawo min ziyara a gida yari>>Inji Barawon Indomie da aka yankewa hukuncin daurin shekaru 2 a gidan yari

Duk Labarai
Wani barawon Indomie, Usman Abdullahi dan shekaru 24 daga jihar Adamawa ya bayyana cewa 'yan matansa 3 da ya rabawa Indomie din daya sata babu wadda ta kai masa ziyara gidan gyara hali. Ya sha Alwashin rabuwa dasu duka da zarar ya fito daga gidan yarin. Ya bayyanawa mai shari'a wannan labari ne yayin da ake sakw duba shari'ar sa. A can baya dai an yanke masa hukuncin daurin shekaru 2 a gidan yari ne. Saidai a yayin ziyara dan rage yawan mazauna gidan yarin, an sake duba hukuncin da aka masa inda a yanzu aka sashi yin shara.
An kama sojojin da aka aika su tsare makarantar ‘yan mata ta jihar Kebbi amma suna koma daukar hoto da ‘yan matan sannan suka tafi yawo

An kama sojojin da aka aika su tsare makarantar ‘yan mata ta jihar Kebbi amma suna koma daukar hoto da ‘yan matan sannan suka tafi yawo

Duk Labarai
Mun Kama Sojojin Da Aka Tura Maga Amma Suka Bar Wurin Aikin Su Har Aka Sace Dalibai, Cewar Minista Matawalle Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa an kama wasu dakarun soji da aka tura makarantar Maga a Jihar Kebbi domin bayar da tsaro, amma suka bar wurin a ranar da 'yan bindiga suka sace ɗalibai mata. Ministan ya ce ana gudanar da bincike don gano ainihin dalilin da ya sa suka bar makarantar a irin wannan lokaci mai haɗari. Ya ƙara da cewa: “Da zarar an kammala bincike, za a ɗauki mataki bisa ka’ida, kamar yadda dokokin soja suka tanada.” Har yanzu dai ana cigaba da fafutukar ganin an ceto daliban da aka sace.
Mu Kiristoci mun san cewa, Abinda Trump ya fada karyane ba mu kadai ake Shyekyewa ba amma maimakon mu gyara masa kuskuren da yayi sai muka amince da abinda ya fada>>Inji Wannan Kiristan

Mu Kiristoci mun san cewa, Abinda Trump ya fada karyane ba mu kadai ake Shyekyewa ba amma maimakon mu gyara masa kuskuren da yayi sai muka amince da abinda ya fada>>Inji Wannan Kiristan

Duk Labarai
Wata Kirista ta fito ta soki 'yan uwanta Koristoci inda tace sun san maganar da shugaban kasar Amirkar Donald Trump yayi ba gaskiya bace amma sun biye masa. Tace kamata yayi su fito su gyarawa Trump Kuskuren da yayi na cewa Kiristane kadai ake Khashewa amma sai suka rika murna da abinda ya fada. Tace Amurka idan ba kowa da kowa zata taimaka a Najeriya ta har taimakonta ba'a so. https://twitter.com/Aashfinn/status/1991899747544936561?t=Ib2aHvCJMljZywEmNJU4vw&s=19
Gwamnatin tarayya ta kulle makarantun Unity, Gwamnatin jihar Katsina ta kulle makarantun Gwamnati, Filato ma an kulle makarantu sai abinda hali yayi

Gwamnatin tarayya ta kulle makarantun Unity, Gwamnatin jihar Katsina ta kulle makarantun Gwamnati, Filato ma an kulle makarantu sai abinda hali yayi

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa Gwamnatin tarayya ta kulle makarantun Unity Schools guda 47 saboda matsalar tsaro. Hakanan daga jihar Filato ma Gwamnatin jihar ta sanar da kulle dukkan marantu sai abinda hali yayi. A jihar Katsina ma an kulle dukkan makarantun Gwamnati sai abinda hali yayi. Hakan na zuwane biyo bayan hare-haren ds ake kaiwa babu kakkautawa kan makarantu. An kai irin wadannan hare-haren akan Makaranta a jihar Kebbi da Jihar Naija.
Kalli Bidiyon: Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma jihar Kebbi da zama kamar yanda shugaba Tinubu ya umarceshi

Kalli Bidiyon: Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma jihar Kebbi da zama kamar yanda shugaba Tinubu ya umarceshi

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa, Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma Jihar Kebbi da zama kamar yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya umarceshi. An ga Ministan ana masa fareti a yayin da ya isa jihar ta Kebbi. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1991914433032147194?t=VBHlg9155qsnwtsAoetBmw&s=19 Hakan na zuwane bayan da aka sace daliban makaranta yara a jihar.