Monday, December 22
Shadow
Wani Rahoto yace An fi shan giya a jihohin Arewa

Wani Rahoto yace An fi shan giya a jihohin Arewa

Duk Labarai
Wani Rahoto daga kafar Statisense yace wai jihohin Arewa ne suka fi shan giya. Rahoton yace jihohin Arewa maso yamma ne akan gaba. Sai jihohin Arewa ta tsakiya na biye musu baya. Sai Jihohin Arewa maso gabas. Sai jihohin Yarbawa na Kudu maso yamma. Sai jihohin Kudu maso kudu. Sai Jihohin Kudu maso yamma. HEAVY ALCOHOL CONSUMERS — 2024 Zone — Male | Female in 1,000 population:North West — 624 | 30 *North Central — 140 | 56North East — 66 | 298South West — 40 | 46South South — 24 | 63South East — 15 | 25 NB : asterisk means insufficient sample size #Statisense(NDHS 2024)
Da Duminsa: Wani Jirgin Sojojin Saman Amurka ya sauka a Najeriya

Da Duminsa: Wani Jirgin Sojojin Saman Amurka ya sauka a Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni daga Abuja sun bayyana cewa wani jirgin sojojin saman Amurka daya taso daga kasar ta Amurka me suna, A US Air Force C-37B ya sauka a Abuja. Jirgin ya saukane a daren jiya. Bayan Awanni 4 Jirgin ya kuma tashi zuwa kasar Ghana. Brant Philip me kawo rahoto akan harkar tsaro a Afrika ne ya ruwaito wannan labari. https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1997243829930561958?t=7g_arf0RZhpWPaLJqC8kHA&s=19
Wani Dan siyasa ne yake sa ana Ghàrkùwà da mutane a Najeriya saboda yana son ya ci zabe haka sukawa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan>>Inji Gwamnan Edo

Wani Dan siyasa ne yake sa ana Ghàrkùwà da mutane a Najeriya saboda yana son ya ci zabe haka sukawa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan>>Inji Gwamnan Edo

Duk Labarai
Gwamnan jihar Edo, Monday, Okpebholo yayi zargin cewa wani dan siyasa ne dake son cin zabe yake sawa ana garkuwa da mutane a Najeriya dan bata sunan Gwamnati. Yace haka sukawa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan kuma sun samu nasara a wancan lokacin. Saidai bai bayyana sunan dan siyasar da yake zargi ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1997230638651347070?t=GKelUTSR6TMChwMlL4O2Aw&s=19
Da Duminsa: Qasar Amurka ta fara kawo màkàmàn da zata yi amfani dasu a Najeriya wajan kai Khàrè-Khàrè

Da Duminsa: Qasar Amurka ta fara kawo màkàmàn da zata yi amfani dasu a Najeriya wajan kai Khàrè-Khàrè

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka ta fara kawo makamai da zata yi amfani dasu wajan hare-haren da zata kai kan kungiyoyin 'yan tà'àddà a Najeriya. Masani kan harkar tsaro, Brant Philip ne ya bayyana haka inda yaje jiragen yaki dauke da makaman sun rika sauka a sansanin da Amurkar ta kafa a kasar Ghana wanda daga canne zata rika kawo harin. Yace Amurkar ta shafe sati 2 kullun tana aiko jirgi mara matuki dan tattara bayanan sirri akan kungiyoyin na ÌŚWÀP da Bòkò Hàràm da sauransu. https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1996848825999241722?t=1J9KQgRJ2ouMkJBiIMq_Iw&s=19
Gwamnatin tarayya ta bayyana sunayen shahararrun masu amfani da kafafen sadarwa da zasu tallata sabuwar dokar Haraji su 20

Gwamnatin tarayya ta bayyana sunayen shahararrun masu amfani da kafafen sadarwa da zasu tallata sabuwar dokar Haraji su 20

Duk Labarai
Kwamitin shugaban kasa dake kula da canja dokar Haraji ya bayyana shahararrun masu amfani da kafafen sada zumunta su 20 da za'a yi amfani dasu wajan tallata sabuwar dokar Haraji Gwamnatin. An fitar da wadannan sunayene daga cikin guda sama da dubu 8 da aka mika sunayensu. Financial Jennifer, Onlinebanker, Don Aza, Mary Efombruh, Baba Ogbon Awon Agba International, Perpetual Badejo, Personalfinancegirl, Tomi Akinwale, Emeka Ayogu, da Aderonke Avava. Sauran sune Odunola Ewetola, Christiana Balogun, Mosbrief, Chidozie Chikwe, Zainulabideen Abdulazeez, Chinemerem Oguegbe, Oyagha Michael, Ayomide Ogunlade, Ayọ̀dèjì Fálétò, and Vera Korie. Saidai a lurar da hutudole yayi dan Arewa ko daya a cikinsu.