Tuesday, December 16
Shadow
Bazan iya zama jam’iyya daya da El-Rufai ba, saboda bashi da akida>>Inji Sanata Wadada yace ya bar jam’iyyar SDP

Bazan iya zama jam’iyya daya da El-Rufai ba, saboda bashi da akida>>Inji Sanata Wadada yace ya bar jam’iyyar SDP

Duk Labarai
Sanata Ahmed Aliyu Wadada daga Jihar Nasarawa ya bayyana cewa ya bar jam'iyyar SDP. Ya bayyana cewa dalilinsa na barin jam'iyyar shine ba zai iya ci gaba da zama da wadanda basu da akida a jam'iyya daya ba. Ya bayyana hakanne a hirarsa da 'yan jarida inda yace Musamman Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, yace bashi da akida. Yace El-Rufai na kan gaba wajan jawo hankalin mutane da cewa ya kamata mulki ya koma kudancin Najeriya. Ya kara da cewa shine ya ce a zabi Tinubu amma saboda bai samu mukamin Minista ba amma ya bar jam'iyyar.
Fasto ya caccaki Shugaba Tinubu daboda fara yakin neman zabe shekaru 2 kamin zabe

Fasto ya caccaki Shugaba Tinubu daboda fara yakin neman zabe shekaru 2 kamin zabe

Duk Labarai
Babban Fasto a jihar Kaduna, Reverend Timothy Yahaya ya caccaki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda ya bayyana cewa, yayi wuri a fara yakin neman zaben. Yace yana kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya dakatar da yakin neman zaben inda yace sai kwanaki 90 kamin zaben ya kamata a fara yakin neman zaben. Reverend Timothy Yahaya yace gaba daya an manta da yiwa mutane aiki inda aka koma yakin neman zabe wanda a baya ba haka tsarin yake ba a kasarnan.
Zulum ya bai wa iyalan sojojin da aka kàshè tallafin miliyan 100

Zulum ya bai wa iyalan sojojin da aka kàshè tallafin miliyan 100

Duk Labarai
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai wa iyalan sojijin da aka kashe da kuma waɗanda aka jikkata a fagen daga a yaƙi da ƴan ta da ƙayar-baya a arewa maso gabas, tallafin naira miliyan 100. Gwamnan ya bayar da tallafin ne ranar Asabar yayin liyafar cin abinci a daidai lokacin da ake ci gaba da bukukuwan sallah, inda babban hafsan sojin ƙasa Laftanar-Janar Olufemi Oluyede da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar suka halarci liyafar a barikin sojoji na Maimalari a Maiduguri. Zulum ya gabatar da chekin kuɗin na naira miliyan 100 ga hannun kwamandan dakarun Haɗin-Kai, Manjo-janar Abdussalam Abubakar. Ya bayyana cewa kowane soja da aka raunata a fagen daga zai samu naira 500,000, yayin da za a raba sauran kuɗin ga iyalan sojojin da aka kashe. Gwamna Zulu...
Gwamnan Benue ya tona Asirin masu daukar nauyin hàrè-hàrèn ‘yan tà’àddà

Gwamnan Benue ya tona Asirin masu daukar nauyin hàrè-hàrèn ‘yan tà’àddà

Duk Labarai
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya zargi wasu ƴan siyasa da ke ci a majalisar tarayya da ɗaukar nauyin hare-hare da ake kai wa jihar, inda ya ce ba za su lamunci hakan ba. Gwamnan ya yi wannan zargi ne yayin tattaunawa a shirin 'Politics Today' na gidan talabijin na Channels. Duk da cewa bai bayyana sunayen ƴan siyasar ba, gwamnan ya ce kwamitin da ya naɗa domin yin binciken kan batun kai hare-haren ya gano akwai sunayen manyan ƴan siyasa, inda ya sha alwashin ɗaukar mataki nan take idan ya karɓi rahoton kwamitin a mako mai zuwa. "Abin takaici yadda wasu manyan ƴan siyasa ke ci gaba da bai wa ƴan bindigar da ke kai hare-haren mafaka da kuma saya musu makamai. Za mu ɗauki mataki tun da ba su damu da irin rayuka da suke salwantar wa ba," in ji gwamna Alia. Jihar ta Benue...
Mun kaiwa masu ikirarin Jìhàdì mummunan hàrì>>Sojojin Najeriya

Mun kaiwa masu ikirarin Jìhàdì mummunan hàrì>>Sojojin Najeriya

Duk Labarai
Sojojin Najeriya sun bayyana cewa, Sun kaiwa Masu ikirarin Jìhàdì mummunan hari ta jirgin sama a kauyen Talala da kauyen Ajigin dake yankin Timbuktu a jihar Borno. Hukumar sojojin tace ta lalata kayan amfanin maharan da yawa. An kai harinne ranar Asabar, 7 ga watan Mayu da misalin karfe 5:30 p.m. Hukumar tace ta kai harinne bayan samun bayanai cewa mayakan masu ikirarin Jihadi na taruwa dan kaiwa sojoji hari. Hukumar tace harin ya tarwatsa maharan inda da yawa suka jikkata kuma shirinsu ya lalace. Hukumar ta yi gargadin cewa, wannan gargadi ne cewa ko a inane makiyansu suke zasu kai musu hari su tarwatsa su.
‘Yan Bìndìgà sun sake kai mummunan hàrì a jihar Arewa

‘Yan Bìndìgà sun sake kai mummunan hàrì a jihar Arewa

Duk Labarai
'Yan Bindiga akalla 10 sun kai mummunan hari wani kauye me suna Chito dake karamar hukumar Ukum ta jihar Benue ranar Asabar. Maharan sun kai harinne da misalin karfe 2:26 am inda suka shafe awanni 2 da mintuna 30 suna aikata masha'a. Ance sun daki mutane da dama sannan suka saci kayan sawa da abinci da sauransu. Daya daga cikin wadanda abin ya shafa, Dr. Isaac H. Mamkaa wanda malamine a kwalejin ilimi ta Katsina Ala ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace 'yan Bindigar sun ce zasu sake komawa su kai musu hari garin.
Ba dan kìyàyyà ga wasu mutanene yasa aka yi yàkìn basasa ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Ba dan kìyàyyà ga wasu mutanene yasa aka yi yàkìn basasa ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa na mulkin Soja, Janar Yakubu Gowon ya bayyana cewa, ba dan kiyayya ga wasu mutanene yasa aka yi yakin basasa ba a Najeriya. Ya bayyana hakane ranar Asabar a Abuja inda yace dalilai na neman hadin kan kasa ne suka sa dole suka fito aka yi yakin basasa dasu. Yakubu Gowon ya bayyana muhimmancin yafiya, da sasanci da hadin kai. Ya bayyana cewa, ya tuna da lokaci mafi wahala a rayuwarsa, watau lokacin yakin basasa, inda yace abu ne da bashi da zabi akansa, kuma yayi abinda ya kamata dan ganin an hada kan kasarnan. Janar Yakubu Gowon dan shekaru 91 yace shima yayi asara a yakin basasa dan kuwa a yakin basasa ne ya rasa babban abokinsa, Major Arthur Unegbe.
A yayin da Kungiyar Dattawan Yarbawa ta Afenifere take kiran a tsige Shugaba Tinubu saboda bai tsinanawa ‘yan Najeriya komai ba, Kungiyar Matasan Yarbawan sun ce basu yadda a tsige shugaban ba

A yayin da Kungiyar Dattawan Yarbawa ta Afenifere take kiran a tsige Shugaba Tinubu saboda bai tsinanawa ‘yan Najeriya komai ba, Kungiyar Matasan Yarbawan sun ce basu yadda a tsige shugaban ba

Duk Labarai
Kungiyar Matasan Yarbawa, (YYSA) tace bata amince da kiran da kungiyar dattawan Yarbawan ta yi ba na cewa a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda yaudarar 'yan Najeriya. Shugaban kungiyar, Olalekan Hammed ne ya fitar da sanarwar ranar Lahadi inda yace zargin da akewa shugaba Tinubu na baiwa kamfanin Mr. Gilbert Chagoury aikin gina titin Legas zuwa Calabar wanda ke da alaka dashi ba gaskiya bane. Yace kamfanin na da tarihin yin ayyuka masu kyau. Yace kiran a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cike yake da siyasa sannan zargin da ake masa bashi da tushe ballantana makama. Sannan yacw shi Tinubu yana duba cancanta ne kamin ya bayar da aiki.
Mutane 9 sun rasu sanadiyyar hadarin mota a jihar Jigawa

Mutane 9 sun rasu sanadiyyar hadarin mota a jihar Jigawa

Duk Labarai
A kalla Mutane 9 ne suka rasu a hadarin mota da ya faru a kauyen Kyaramma dake karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa. Hukumar 'yansandan jihar ta tabbatar da faruwar hadarin inda tace ya farune da misalin karfe 2 na yamma tsakanin wasu motocin Golf 3 guda biyu wanda kuma ya bar mutane da yawa sun jikkata. Kakakin 'yansandan jihar, Shiisu Adam ne ya bayyana hakan inda yace motocin sun yi taho mu gama, yace bayan hadarin 'yansandan sun kai dauki wajan inda suka kai wadanda suka jikkata Asibiti. Kwamishinan 'yansandan jihar, CP A.T. Abdullahi, ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan mamatan inda yace direbobi su rika kiyaye dokokin hanya dan gujewa hadarin.