Sunday, February 15
Shadow
Kalli Bidiyon: Wani dan Najeriya da ya je kallon wasan AFCON a kasar Morocco na mamakin cewa a karin farko ya ga an dauke wutar lantarki a kasar

Kalli Bidiyon: Wani dan Najeriya da ya je kallon wasan AFCON a kasar Morocco na mamakin cewa a karin farko ya ga an dauke wutar lantarki a kasar

Duk Labarai
Wani dan Najeriya da ya je kasar Morocco kallon wasan AFCON ya bayyana mamakinsa bayan ganin a karon farko an dauke wuta a kasar. Ya rika ihun cewa a karin farko NEPA sun dauke wuta a kasar ta Morocco. Wasu dai sun rika bayyana cewa hakan alamar Nasara ce ga Super Eagles. https://twitter.com/i/status/2010823217187893698
An kama daliban jami’ar AAU dake jihar Edo su 50 saboda sun yi zàngà-zàngàr kokawa da matsalar tsaro

An kama daliban jami’ar AAU dake jihar Edo su 50 saboda sun yi zàngà-zàngàr kokawa da matsalar tsaro

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa an kama daliban jami'ar AAU kusan 50 saboda sun yi zanga-zangar neman kawo karshen matsalar tsaro. Bidiyon daliban cunkushe a cikin mota ya dauki hankula sosai inda aka gansu jami'an tsaro sun kamasu sun tafi dasu zuwa kotu. Lamarin ya dauki hankula inda akai ta muhawara akai. https://twitter.com/i/status/2010815658578047091
Kalli Bidiyon: Ku a ganinku dadi Muke ji a matsayin mu na Gwamnoni koh, Toh wahala muke sha>>Inji Gwamnan Katsina Dikko Radda

Kalli Bidiyon: Ku a ganinku dadi Muke ji a matsayin mu na Gwamnoni koh, Toh wahala muke sha>>Inji Gwamnan Katsina Dikko Radda

Duk Labarai
Gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Radda ya bayyana cewa, mutane na ganin dadi suke ji a mulki idan an ga sun hau Mota ko sun hau jirgi. Gwamnan yace wahala ce saboda idan sun je kasashen wajen ba abinda suke so suke aikatawa ba. Yace taruka ne daga wannan sai wannan. Gwamnan ya kara da cewa, Amma su suka saya tunda su suka nemi shugabancin kuma Allah ya basu. https://twitter.com/i/status/2010737367980843180
‘Yan majalisar jihar Rivers 2 sun ce sun janye daga yunkurin tsige Gwamna Fubar

‘Yan majalisar jihar Rivers 2 sun ce sun janye daga yunkurin tsige Gwamna Fubar

Duk Labarai
'Yan majalisar jihar Rivers 2 sun bayyana janyewa daga yunkurin tsige gwamnan jihar, Simi Fubara. 'Yan majalisar sun ce sun dauki wannan matakine biyo bayan kiraye-kirayen dattawa a ciki da wajen jihar ta Rivers su canja matsayarsu. Sun ce duk da gwamnan yayi laifi na karya dokar kundin tsarin mulki amma suna kira ga abokan aikinsu da su duba au sassauta a janye wannan matsaya. https://twitter.com/i/status/2010740601885741243
Dangote ya wadatar da Najeriya da man fetur, Mun daina shigo da man fetur daga kasashen waje>>Inji ‘Yan kasuwar man fetur

Dangote ya wadatar da Najeriya da man fetur, Mun daina shigo da man fetur daga kasashen waje>>Inji ‘Yan kasuwar man fetur

Duk Labarai
A karshe dai bayan dambarwar da akai ta yi tsakanin 'yan kasuwar man fetur da Dangote, 'yan kasuwar a yanzu sun ce sun yadda Dangote ya wadatar da Najeriya da man fetur din. Sun sha Alwashin daina shigo da man daga kasashen waje. Hakan na nufin Dangote zai zama me wuka da nama akan harkar man fetur a Najeriya.