Thursday, December 18
Shadow
An kama matashi da ya kkàshè Budurwarsa

An kama matashi da ya kkàshè Budurwarsa

Duk Labarai
Mahukunta a jihar Legas sun kama wani mutum me suna Gbolahan Adebayo bida zargin kashe budurwarsa. Adebayo dan shekaru 23 ya daki budurwarsa me shekaru 25 har ta mutu. Lamarin ya farune a ranar 21 February 2025 kamar yanda Daily Post ta ruwaito. Kakakin 'yansandan jihar, Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace abin ya farune a Ijedodo, Isheri-Osun dake jihar. Wani makwabci daya shaida lamarin yace ya ji Adebayo na dukan budurwar tasa kuma da aka leka aka tarar bata motsi, saidai zuwa yanzu ba'a san dalilin da yasa ya kashe budurwar tasa ba. Tuni dai aka kai ta Asibiti inda likitoci suka tabbatar da ta mutu.
Haduwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr da shahararriyar me yin fina-finan bàtsà Mìa Khàlìfà ya jawo cece-kuce

Haduwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr da shahararriyar me yin fina-finan bàtsà Mìa Khàlìfà ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Tauraruwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr ta hadu da shahararriyar me fina-finan batsa, watau Mia Khalifa. Bidiyon haduwarsu suna hira ya karade kafafen sada zumunta inda wasu ke tambayar me ya hadasu? Mia Khalifa dai wadda asalinta 'yar kasar Lebanon ce ta bayyana daina yin fina-finan batsa, inda ta koma shafin Onlyfan wanda saidai idan mutum nason ta mai bidiyon ta tsirara ya biya kudi ta masa.
Bidiyo:Na Tuba na daina Yada Badala>>Inji ‘Yar Tiktok, Shalele

Bidiyo:Na Tuba na daina Yada Badala>>Inji ‘Yar Tiktok, Shalele

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok da ta shahara sosai wajen yada badala da maganganun batsa Shalele ta bayyana cewa ta tuba. Shalele wadda har bidiyoyinta tsirara sun yadu sosai tace daga yau ta daina duk wani na ba daidai ba da ya sabawa Addini da Al'ada. https://www.tiktok.com/@drshalele2/video/7473392723249106231?_t=ZM-8uCdD1ruVtv&_r=1 Da yawa sun jinjina mata kan wannan mataki data daukarwa rayuwarda.
Dan Allah ku gayawa El-Rufai ya shafa min Lafiya, Ni Aiki nane a gabana ba cece-kuce a gidajen watsa labarai ba>>Nuhu Ribadu

Dan Allah ku gayawa El-Rufai ya shafa min Lafiya, Ni Aiki nane a gabana ba cece-kuce a gidajen watsa labarai ba>>Nuhu Ribadu

Duk Labarai
Ba Zan Yi Musayar Yawu Da Nasir El-Rufai Ba, Cewar Nuhu Ribadu "An ja hankalina zuwa ga hirar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya yi da kafar yada labarai da yammacin ranar Litinin. Da ba don gudun kada na yi shiru a gaskata maganganunsa ba, da na yi watsi da shi. Saboda na fi shagaltuwa da tarin aiyukan da ke gabana,fiye da tanka ire-iren su Nasir El-Rufai a kafafen yada labarai. Duk da cin zarafi da aibata ni da Nasiru yake yi, hakan bai sa na taba fadin wani mummunan abu akansa ba a ko’ina. Ba don komai na ki aibata shi ba sai don mutunta zumuncin da ke tsakaninmu da kuma abotar mu ta baya, don haka abinda ban yi tun a baya ba, ba zan fara yanzu ba. Sai dai ina kira ga jama'a da su yi watsi da ikirarin El-rufai akaina Bari na kankare muku shakku in fadi...
Nuhu Ribadu na son zama shugaban kasa a 2031 bayan Tinubu ya gama shiyasa yake son bata min suna>>El-Rufai

Nuhu Ribadu na son zama shugaban kasa a 2031 bayan Tinubu ya gama shiyasa yake son bata min suna>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, Nuhu Ribadu na son zama shugaban kasa a shekarar 2031 bayan Tinubu ya gama Mulki. Yace shiyasa ma Nuhu Ribadun ya hada kai da gwamnan Kaduna na yanzu, Malam Uba Sani dan bata masa suna. El-Rufai ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Inda ya kara da cewa amma kokarin na bata masa suna yana basu wahala.
Da Tinubu ya zarce a 2027 gara ma koda daga kudu ne a sake samun wani ya zama shugaban kasa>>El-Rufai

Da Tinubu ya zarce a 2027 gara ma koda daga kudu ne a sake samun wani ya zama shugaban kasa>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa gara wani daga kudu ya sake zama shugaban kasa da Tinubu ya sake zama shugaban kasa a shekarar 2027. El-Rufai ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Yace bai da tabbacin nan da lokacin zaben 2027 ko zai ci gaba da dama a Jam'iyyar APC. El-Rufai ya zargi Tinubu da nada yaransa mafi yawanci yarbawa a mukaman siyasa.
Karamin yaro dan shekaru 4 ya kkàshè kansa ta hanyar hàrbìn kansa da Bìndìgàr iyayensa da yake wasa da ita a cikin mota

Karamin yaro dan shekaru 4 ya kkàshè kansa ta hanyar hàrbìn kansa da Bìndìgàr iyayensa da yake wasa da ita a cikin mota

Duk Labarai
Karamin yaro me shekaru 4 ya harbi kansa da Bindigar iyayensa da ya dauka a mota. Rahoton yace yaron ya harbi kansa a kai ne. Lamarin ya farune a Davenport dake jihar Floridan kasar Amurka. Iyayen yaron Robert Morris da matarsa, Quinta Morris suna shiri ne dan kai 'ya'yansu zuwa cin Pizza inda shi yaron doki ya kaishi ga har ya rika kowa shiga mota ya zauna yana jiran iyayensa su je. Matar tana kan Kwamfuta a yayin da Mijin yake bandaki yana wanka a yayin da lamarin ya faru, matar tace ta ji karar abu inda ta yi tsammanin yaranta ne ke kwaramniya. Ta leka dan ta musu magana amma sai ta tarar da danta me shekaru 11 da me shekaru 7 ne kawai suke wasa. Tan sai ta hango kofar shiga garejin motarsu a bude aikuwa tana lekawa sai ta ga dan nata a kwance, da harbin bindiga akai....

Dalilin da yasa Tinubu yaki baka Minista shine ka taba zagin Annabi Isa(AS), sannan An zarge ka da hannu a kkàshe ‘yan Shi’a, sannan kuma ka yi barazanar kkàshè Turawa>>Reno Omokri ya mayarwa da El-Rufai Martani

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri ya bayyana dalilan da suka sa Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bai tsallake tantancewar zama minista da majalisa ta masa ba. Wannan martani na zuwa bayan da El-Rufai a hirar da yayi da gidan talabijin na Arise TV yace ba majalisa ce taki tantanceshi ba, Tinubu ne ya canja ra'ayi game da mukamin da yaso ya bashi. Reno Omokri wanda a yanzu ya shiga sahun masu kare gwamnatin Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa majalisar tarayya ta gudanar da bincike a cikin gida da kasashen waje kan Nasir El-Rufai kuma binciken nasa bai yi kyau ba shiyasa ba'a bashi mukamin ministan ba. Ya jero laifukan El-Rufai da suka hana a bashi mukamin ministan kamar haka: Yace a ranar Alhamis, February 7, 2019 El-Rufai ya yiwa Turawa masu sa ido...
NAFDAC sun kulle shagunan dake sayar da magungunan jabu

NAFDAC sun kulle shagunan dake sayar da magungunan jabu

Duk Labarai
Hukumar kula da ingancin magunguna da abinci ta Najeriya Nafdac ta ce ta rufe sama da shaguna 11,000 tare da kama mutum 40 a yaƙin da take yi da sayar da ƙwayoyin jabu. Da take yi wa 'yanjarida jawabi a ranar Lahadi, shugabar hukumar Farfesa Mojisola Adeyeye ta ce sun tsara samamen ne tun shekara ɗaya da ta wuce. Zuwa yanzu, Nafdac ta kai samame kasuwanni da dama ciki har da Idumota a Legas, da Ariaria a garin Aba, da Bridge Market a Onitsha a ranar 10 ga watan Fabrairu. Ta ce sun hari kasuwanni uku da ke rarraba kashi 80 cikin 100 na magunguna a Najeriya, kuma sun yi nasarar kamawa tare da ƙwace ƙwayoyin jabu da waɗanda ba a yi wa rajista ba. Farfesar ta kuma sun samu sama da mota 20 ta jabun magunguna a Aba, aƙalla 30 a Onitsha, da wasu 27 a kasuwar Idumota. "Abin da muka ...