Wednesday, December 17
Shadow
An kama mutane 2 a jihar Borno saboda Kkashe wata mata bisa zargin Maita

An kama mutane 2 a jihar Borno saboda Kkashe wata mata bisa zargin Maita

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Borno sun sanar da kama mutane 2 bisa zargin kisan da sukawa wata mata me shekaru 70 a Biu dake jihar bayan zarginta da maita. Kakakin 'yansandan jihar, CP Yusuf Lawan ya tabbatar da faruwar lamarin a sanarwar da ya fitar ranar Asabar, 22 ga watan Fabrairu 2025. Ya bayyana sunayen wadanda ake zargi kamar haka,Ja’o Muhammad, Idrisa Muhammad, 20, da Ya’u Muhammad, 30.  Yace matar sunanta Hajara Saleh wadda aka kashe a Bantine dake Biu. Hukumar 'yansandan tace mutanen da ake zargin sun hada kai dan kashe Hajara inda suka zargeta da maita da jawowa garinsu bala'i. Ya bayar da tabbacin hukunta wadanda ake zargin.
Zamu doke APC da PDP a 2027, Kwankwaso ne zai zama shugaban kasa>>Inji Jam’iyyar NNPP

Zamu doke APC da PDP a 2027, Kwankwaso ne zai zama shugaban kasa>>Inji Jam’iyyar NNPP

Duk Labarai
Jam'iyyar NNPP ta bayyana cewa a zaben shekarar 2027 zata doke Jam'iyyun APC da PDP. Shugaban Jam'iyyar, Dr. Ajuki Ahmad ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Abuja inda yace zasu yi nasarar hakanne ta hanyar jagoransu, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso wanda shine zai zama shugaban kasar Najeriya a 2027 Duk da rikicin cikin gida da ya mamaye Jam'iyyar ta NNPP, Dr. Ajuki Ahmad yace a yanzu sun samu zaman lafiya a cikin Jam'iyyar. Yace duk da yake hakan ba abune me sauki ba amma sun sha Alwashin cimma burinsu inda yace zasu fitar da Najeriya daga halin data tsinci kanta a ciki.
Ji yanda Jirgin saman Sojin Najeriya ya kkàshè ‘yan Bìndìgà 23 a jihar Zamfara

Ji yanda Jirgin saman Sojin Najeriya ya kkàshè ‘yan Bìndìgà 23 a jihar Zamfara

Duk Labarai
Jirgin yaki na sojojin Najariya ya kashe 'yan Bìndìgà 23 a garin Tsafe dake jihar Zamfara. An kashe 'yan Bindigar ne a wannan karshen makon da muke ciki. Rahotanni sun bayyana cewa 'yan Bindiga da yawa dake karkashin dan Bindiga Ado Aleiro sun bar tsafe inda suka tafi dan kai hari da satar shanu a wasu kauyuka. Rahoton yace 'yan Bindigar sun yi nasarar kwace shanun duk da mutanen garin sun dan musu Turjiya, a yayin da suke kokarin guduwa da shanun ne sojojin Najariya suka gansu suka bude musu wuta. Shaidu sun bayyana cewa an kashe 'yan Bindigar da yawa inda wasu suka ce sun ga gawarwakin 23 daga cikinsu. Daga baya dai sojojin sun kwace shanun da 'yan Bindigar suka kwato.
Dalilin da yasa na kifar da gwamnatin Buhari duk da yake cewa nine shugaban ma’aikatansa>>IBB ya magantu

Dalilin da yasa na kifar da gwamnatin Buhari duk da yake cewa nine shugaban ma’aikatansa>>IBB ya magantu

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida,IBB ya bayyana dalilin da yasa ya kifar da Gwamnatin tsohon shugaban kasa, Janar Muhammadu Buhari. Ya bayyana hakane a littafinsa da ya wallafa wanda yayi bayani kan yanda ya gudanar da aikinsa. IBB wanda shine shugaban ma'aikatan Gwamnatin Buhari a wancan lokacin yace bai gamsu da yanda Buhari ke gudanar da mulki ba shiyasa ya masa juyin mulki. IBB yace tare suke mulki amma sam yaga tsare-tsaren Buhari basa kawo ci gaba a kasar shiyasa ya kifar dashi a shekarar 1985.
Kalli Bidiyo: Rawar da Ali Nuhu ya tika da Rahama Sadau ta sa ana ta cece-kuce inda wasu ke cewa, wai yaushe zai girma?

Kalli Bidiyo: Rawar da Ali Nuhu ya tika da Rahama Sadau ta sa ana ta cece-kuce inda wasu ke cewa, wai yaushe zai girma?

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Ali Nuhu Sarki ya dauki hankula sosai a wajan bikin Arewa Turnup da Rahama Sadau ta shirya. Babban abinda ya dauki hankalin mutane shine yanda Ali Nuhu da Rahama Sadau suka rika rawa tare da Umar M. Shariff. Ali Nuhu ya saki jikinsa sosai yayi rawa ba tare da shakka ba. Hakan yasa mutane ke cewa wai yaushe zai girma ne? https://www.tiktok.com/@goldenbackup1/video/7474538141509078277?_t=ZM-8u9bdVISxtd&_r=1 Ali Nuhu dai ya saba rawa irin haka, saidai mutane sun kasa sabawa da ganinsa yana rawar inda a duk sanda yayi sai an yi magana.
Wani mùtùm ya mùtù a kokarin dakko wayarsa data fada rijiya

Wani mùtùm ya mùtù a kokarin dakko wayarsa data fada rijiya

Duk Labarai
Wani mutum me suna Sunday Jimoh a jihar Ogun ya mutu a kokarin dakko wayarsa data fada rijiya. Mutumin me shekaru 31 na zaunene a Laditan dake yankin Oja-Odan na jihar, kuma lamarin ya farune ranar 22 ga watan Fabrairu da misalin karfe 10: 00 na safe. Kakakin 'yansandan jihar, CSP Omolola Odutola ya tabbatar da faruwar lamarin a sanarwar da ya fitar ranar Lahadi. Wata mata Kabiru Aladeshayi Ayigbere ce ta kaiwa 'Yansandan korafi akan lamarin inda tace an yi kokarin hana Jimoh shiga rijiyar amma ya nace sai ya shiga. Omolola yace sun je wajan inda aka ciro gawar mamacin kuma an yi bincike babu wata alamar duka a jikinsa wanda hakan ya tabbatar da cewa mutuwa yayi ta Allah da Annabi. Danginsa sun bukaci a basu gawarsa su binneshi kamar yanda addinin musulunci ya tanada kuma an...
Wata Sabuwa: Masanin Kimiyya yace mafi yawan mutane zasu so yin Luwadi da Madigo idan suka samu damar yin hakan a bincikensa

Wata Sabuwa: Masanin Kimiyya yace mafi yawan mutane zasu so yin Luwadi da Madigo idan suka samu damar yin hakan a bincikensa

Duk Labarai
Wani masanin kimiyya a kasar Ingila me suna Dr Jason Hodgson ya yi ikirarin cewa, mafi yawan mutane na da son aikata luwadi da madigo idan suka samu damar yin hakan. Ya bayyanawa jaridar mailonline cewa duk da yake wadanda suka fito suka bayyana cewa su 'yan Luwadi da madigo ne basu da yawa amma akwai masu irin wannan dabi'ar da yawa dake boyewa. A cewarsa, idan wasu suka samu dama, suma zasu so aikata irin waccan masha'a. Yana bayyana cewa, wannan dabi'a ce ta mafi yawan mutane tsakanin maza da mata wadda ke cewa bisexual watau mace tana son namiji sannan tana son mace 'yar uwarta, hakanan namiji yana son mace amma kuma yana son namiji dan uwansa. Saidai da yawa ko da a cikin Turawan sun karyata wannan masanin kimiyya inda suka ce kawai yana son yada badala ne kuma abinda ya f...
Shari’ar da ake min yaudarace, Gara ma in mùtù a daure kawai, ba zan kara zuwa kotu ba>>Nnamdi Kanu ya magantu

Shari’ar da ake min yaudarace, Gara ma in mùtù a daure kawai, ba zan kara zuwa kotu ba>>Nnamdi Kanu ya magantu

Duk Labarai
Shugaban haramtaciyyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu dake daure ake zarginsa da cin amanar kasa ya sha Alwashin ba zai kara zuwa kotu ba. Kanu ya bayyana hakane inda yace shari'ar da ake masa yaudara ce kawai. Kanu yace dalili daya zai sashi ya ci gaba da zuwa kotu shine idan za'a gurfanar dashi a gaban kotun dake da cikkakken ikon a kudin tsarin mulkin Najeriya. Kanu ya kawo dalilai da yawa da yace yana ga kotunan da ake kaishi a yanzu ba zasu iya masa hukuncin da ya dace ba.