Tuesday, December 16
Shadow
Sojojin mu sun yi kadan, Muna bukatar sojoji Dubu dari biyar kamin mu iya magance matsalar tsaro a Najeriya>>Janar Din soja ya koka

Sojojin mu sun yi kadan, Muna bukatar sojoji Dubu dari biyar kamin mu iya magance matsalar tsaro a Najeriya>>Janar Din soja ya koka

Duk Labarai
Janar din soja, Maj-Gen Pat Akem-Vingir (retd), ya bayyana cewa, ana bukatar karin sojoji a Najeriya muddin ana son sojojin su iya magance matsalar tsaron da ake da ita. Ya bayyana hakane a hirar da gidan talabijin na ChannelsTV suka yi dashi inda yace a yanzu sojoji 230,000 ne Najeriya ke dasu. Yace yawanci nasarorin da suka samu a Arewa Maso gabas akan B0K0 Hàràm an samu koma baya saboda kungiyar ta sake komawa ta kwace guraren da aka kwace daga gurinta. Yace dan haka akwai bukatar kara yawan sojojin da ake dasu zuwa 500,000 idan ana son dawwamar da nasarar tsaro da ake samu. Tsohon Janar din yace kuma Gwamnati ta daina kula sabuwar kungiyar masu tada kayar baya ta Lakurawa inda yace karamar kungiyace wadda za'a iya yin maganinta a lokaci guda, yace bai kamata ana maganarsu b...
Hotuna: Dansandan Najeriya me mukamin ASP ya kkashe kansa a jihar Naija

Hotuna: Dansandan Najeriya me mukamin ASP ya kkashe kansa a jihar Naija

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, dansandan Najeriya me mukamin ASP ya kashe kansa a jihar Naija. Dansandan me suna shafi'u Bawa na tare da runduna ta 61 ce dake Kontagora a jihar Naija kuma wata majiya ta bayyanawa jaridar Daily Trust cewa ya kashe kansa ne ranar Asabar da yamma. An tarar gawarsa na reto ne a dakinsa da ya sagale kansa a jikin silin. Rahotanni sunce mahaifinsa, Mallam Usman Bawa ne ya fara kai rahoton mutuwar dan nasa a ofishin 'yansanda dake Kontagora. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an baiwa danginsa gawar inda kuma aka fara bincike akan lamarin.
Ko da dalibi ya ci jarabawar JAMB ba tabbacin zai samu admission a jami’a>>Inji Hukumar JAMB

Ko da dalibi ya ci jarabawar JAMB ba tabbacin zai samu admission a jami’a>>Inji Hukumar JAMB

Duk Labarai
Hukumar shirya jarabawar shiga jami'a ta JAMB ta bayyana cewa, ko da dalibi ya ci jarabawar ta JAMB to ba lallai ya sami damar shiga jami'a ba. Me magana da yawun hukumar, Fabian Benjamin ne ya bayyana haka a ranar Lahadi, 9 ga watan Fabrairu inda yace samun damar shiga jami'a na bukatar mutum ya samu sakamako na kammala sakandare me kyau da JAMB din da kuma Post UTME. JAMB ta bayar da wannan amsa ne bayan da iyaye ke ta korafin cewa 'ya'yansu na rubuta jarabawar JAMB kuma suna ci amma ba'a basu damar shiga jami'a. Ya kawo misalin wasu iyaye da suka yi korafin an hana 'ya'yansu shiga jami'a a jihohin Filato da Cross River amma yace daga baya da aka musu bayani sai suka gane cewa 'ya'yan nasu ne basu cancanci shiga jami'ar ba. Ya kuma jawo hankalin iyaye dasu fahimci tsarin baya...
Ya kamata a rage zagin da ake min a rika godemin domin gaba dayan kudaden da aka samu daga cire tallafin Man fetur na rabar dasu ga ‘yan Najeriya>>Shugaba Tinubu

Ya kamata a rage zagin da ake min a rika godemin domin gaba dayan kudaden da aka samu daga cire tallafin Man fetur na rabar dasu ga ‘yan Najeriya>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bukaci 'yan Najeriya su rage sukar da suke masa maimakon hakan, su rika gode masa. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin me bashi shawara ta musamman akan mazabu, Khadija Omotayo inda ta wakilceshi a Birnin Jos na jihar Filato wajan taron karawa juna sani da ya gudana a ranar Asabar. Khadija tace, shugaban kasar ya cire tallafin man fetur ne dan amfanin kowa, domin kuwa kudaden da aka samu daga cire tallafin man fetur din an rabasu ga kowace jiha ta hannun gwamnoni. Tace shugaban kasar ya kuma karawa ma'aikata Albashi sannan yace zai kara yin wani karin, tace gashi ya turata ta wakilceshi a taron a jihar da Jam'iyyar PDP ke shugabanci wanda hakan na nuna bashi nuna wariya kowa nashine, tace dan haka shugaban ya cancanci yabo. Khadija ta kuma ba...
Kalli Hotuna: Yanda sojojin Najariya suka kafa tutar Najeriya bayan kwace iko da maboyar ‘yan Bìndìgà

Kalli Hotuna: Yanda sojojin Najariya suka kafa tutar Najeriya bayan kwace iko da maboyar ‘yan Bìndìgà

Duk Labarai
Sojojin Najaria sun kafa tutar Najeriya bayan kwace iko da wata maboyar 'yan Bindiga a jihar Zamfara. Sojojin dai sun dage da matsawa 'yan Bindiga inda suka kashe da dama wasu kuma suka tuba suka mika makaman hannunsu. Nasara ta kwanannan da sojojin suka samu itace wadda suka kai Ruwan Kunku inda suka kone gidajen 'yan Bindigar.
Kalli Bidiyo: Dan Siyasar APC ya sha Ihun bama so sannan aka koreshi a jihar Katsina bayan da ya je yakin neman Zabe

Kalli Bidiyo: Dan Siyasar APC ya sha Ihun bama so sannan aka koreshi a jihar Katsina bayan da ya je yakin neman Zabe

Duk Labarai
Shugaban kungiyar shuwagabannin kananan hukumomi ta Najeriya kuma shugaban karamar hukumar Kaita, Bello Lawal 'Yandaki wanda dan Jam'iyyar APC ne ya sha ehon bama so sannan aka koreshi daga kauyen 'Yanhoho bayan da ya je yakin neman zabe. Bello ya je yakin neman zabe ne a karo na biyu kauyen saidai ya gamu da fushin jama'ar yankin inda suka taru suka fasa masa gilasan mota sannan suka koreshi suna yi masa ihu. A bidiyon da ya watsu sosai a kafafen sadarwa, an ga matasan 'yanhoho da itace suna ihun basa so da sauransu. Kalli bidiyon anan
Fina-Finan da ‘yan Najeriya ke kallone yasa mutane da yawa ke son yin kudi dare daya>>Inji Matar Shugaban kasa, Remi Tinubu

Fina-Finan da ‘yan Najeriya ke kallone yasa mutane da yawa ke son yin kudi dare daya>>Inji Matar Shugaban kasa, Remi Tinubu

Duk Labarai
Matar shugaban kasa, Sanata Remi Tinubu ta bayyana cewa, fina-finan Nollywood da kafafen sada zumunta da 'yan Najeriya ke ta'ammuli dasu ne ke zuga da wa wajan son yin kudi dare daya. A cikin abubuwan da take suna zuga mutane dan neman kudin dare daya hadda Addini. Tace Hakan ne ma yake sa ake safarar mutane inda tace tana baiwa hukumar hana safarar mutane gwarin gwiwa akan aikin da take. Ta bayyana hakane yayin da shugabar NAPTIP Binta Bello ta kai mata ziyara a ofishinta dake fadar shugaban kasa a Abuja. Me taimakawa matar shugaban kasar ta bangaren yada labarai, Busola Kukoyi ce ta bayyana haka a wata sanarwa data fitar inda tace Matar shugaban kasar ta bada shawarar a rika karfafa mutane dan su rika yin aiki tukuru da kuma hakuri da rayuwa.
Wanda suka yi Gàrkùwà da janar Tsiga a Katsina sun nemi a biya kudin fansa Naira Miliyan dari biyu da hamsin(250m)

Wanda suka yi Gàrkùwà da janar Tsiga a Katsina sun nemi a biya kudin fansa Naira Miliyan dari biyu da hamsin(250m)

Duk Labarai
' Yan Bindigar da suka yi garkuwa da tsohon janar din soja kuma tsohon shugaban hukumar bautar kasa(NYSC) Janar Maharazu Tsiga rtd sun nemi a biya Naira Miliyan 250M a matsayin kudin fansarsa. Wata majiya dake kusa da iyalan janar dinne suka bayyana hakan inda suka ce masu garkuwa da mutanen sun kira iyalan janar din suka sanar da hakan. An yi garkuwa da janar tsiga ne tare da wasu mutane 9. Lamarin ya faru ranar Laraba da dare inda 'yan Bindiga su kusan 100 suka zagaye gidansa suka tsafi dashi. Dan majalisar tarayya dake wakiltar Bakori da Danja ya tabbatar da faruwar lamarin saidai zuwa yanzu hukumomin soji dana 'yansanda basu bayar da ba'a si ba kan lamarin.
An gurfanar da tsohon Minista kuma tsohon dan takarar shugaban kasa Kabiru Turaki a kotu bisa zargin yin lalata da wata mata har ta kai ga ya dirka mata ciki

An gurfanar da tsohon Minista kuma tsohon dan takarar shugaban kasa Kabiru Turaki a kotu bisa zargin yin lalata da wata mata har ta kai ga ya dirka mata ciki

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja na cewa, an gurfanar da tsohon Ministan ayyukan na musamman Kabiru Turaki (SAN) a kotun magistre dake Abuja bisa zargin yin lalata da wata mata. Saidai Turaki ya musanta zargin da ake masa bayan da aka karanto masa zarge-zargen a gaban me shari'a, Abubakar Jega. An zargi ministan da cewa a tsakanin watan Disamba na shekarar 2014 zuwa watan August na shekarar 2016 ya kai wata me suna  Ms. Hadiza Musa wani otal me suna Hans Palace inda yayi lalata da ita. Ya kuma sake yin lalata da matar a otal din Ideal Home Holiday dake Asokoro tsakanin watan August 2016 zuwa watan November 2021. Daga baya ma sai ya kama mata gida dake da adireshin at No. 12 Clement Akpagbo Close, Gauzape inda ya ci gaba da lalata da ita da sunan cewa ya aureta. A ...
Maganar canja tsarin karatun Najeriya daga JSS da SSS zuwa shekaru 12 ba gaskiya bane>>Inji Gwamnatin Tarayya

Maganar canja tsarin karatun Najeriya daga JSS da SSS zuwa shekaru 12 ba gaskiya bane>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Ma'aikatar ilimi ta tarayya, ta bayyana cewa, Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya bada shawarar canja tsarin karatun Najeriya daga JSS da SSS zuwa shekaru 12 ne amma bai ce an canja ba. Sanarwar tace maganar canja tsarin kai tsaye ba gaskiya bane. Me magana da yawun ma'aikatar Ilimin, Folasade Boriowo ta bayyana cewa, kwamitin Ilimi na kasa zai duba wannan shawara kamin sanin matakin da ya kamata a dauka na gaba. Ministan ya bayar da wannan shawara ne a Abuja ranar 6 ga watan Fabrairu a wajan wani taro kan Ilimi da aka yi a Abuja.