Saturday, April 11
Shadow
Duk da farashin Danyen Man fetur ya fadi a kasuwanin Duniya, ‘yan kasuwar Man fetur na Najeriya sun bayyana dalilin da farashin man fetur din yaki sauka a Najeriya

Duk da farashin Danyen Man fetur ya fadi a kasuwanin Duniya, ‘yan kasuwar Man fetur na Najeriya sun bayyana dalilin da farashin man fetur din yaki sauka a Najeriya

Duk Labarai
Kungiyar masu tace man fetur na Najeriya, CORAN sun bayyana dalilin da yasa farashin man fetur ya ki sauka a Najeriya duk da farashin danyen man fetur ya sauka a kasuwannin Duniya. Sakataren yada labarai na CORAN, Eche Idoko ya bayyana cewa, dillalai dake tsakanin masu saye da masu sayar da man fetur dinne ke kawo matsalar hana farashin tashin sauka a Najeriya. Tun a makon da ya gabata ne dai muka kawo muku rahoton cewa, farashin na danyen man fetur a kasuwar Duniya ya sauka zuwa dala $65. Saidai a Najeriya, farashin ya ki sauka, da yake ci gaba da bayani, sakataren CORAN, Eche Idoko yace, idan ba dawo da ci gaba da sayarwa masu tace man fetur danyen man fetur din aka yi da kudin Naira ba, farashin man fetur din zai ci gaba da tashi ne. Yace amma matsalar itace, dillan man fet...
Kalli Bidiyo: Bansan Iya mazan da suka yi lalata dani ba bayan da mijina ya sakeni>>Inji Wannan Bazawarar

Kalli Bidiyo: Bansan Iya mazan da suka yi lalata dani ba bayan da mijina ya sakeni>>Inji Wannan Bazawarar

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A cikin irin bidiyon live din Y America dake ci gaba da yaduwa a kafafen sadarwa na Tiktok an ji inda yayi hira da wata Bazawara. Matar ta bayyana cewa, ita 'yar jihar Borno ne kuma mijinta ne ya fara saninta a matsayin 'yan mace. Amma bayan da ta fita daga gidansa, mazan da suka yi lalata da ita suna da yawa. Saurari bidiyon anan: https://www.tiktok.com/@screenrecord41/video/7474964943503101206?_t=ZM-8vJq9AiCkTP&_r=1 Me zaku ce akan wannan?
Za’a biya matasa da suka kammala Bautar Kasa karin kudin Naira 77,000>>Inji Hukumar NYSC

Za’a biya matasa da suka kammala Bautar Kasa karin kudin Naira 77,000>>Inji Hukumar NYSC

Duk Labarai
Shugaban hukumar NYSC ta bautar kasa, Brigadier General Olakunle Nafiu ya bayar da tabbacin cewa, matasan da suka kammala bautar kasa na karshe zasu samu karin Alawus din da aka yi na Naira 77,000. Ya bayyana hakane ranar Alhamis a Abuja wajan wani taron wayarwa da juna kai. Sai a watan da ya gabata ne dai aka fara biyan matasan masu bautar kasa karin kudin 77,000 duk da cewa tun watanni 8 da suka gabata, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanyawa dokar karin mafi karancin Albashi hannu. Ya bayyana cewa zasu biya matasan da suka gama kwanannan bashin da suke bi na karin 77,000 da aka yi. Yace da zarar sun samu kudin, zasu biya matasan dan suna da bayanansu na banki.
Kalli Bidiyon yanda matasa suka tsinci Container cike da kaji da igiyar ruwa ta jawo gabar Teku

Kalli Bidiyon yanda matasa suka tsinci Container cike da kaji da igiyar ruwa ta jawo gabar Teku

Duk Labarai
Wasu matasa a kasar Jamaica dake Nunkaya a gabar Teku sun yi tsintuwar wata Container cike da kaji. Igiyar ruwa ce dai ta kai Container wanda manyan jiragen ruwa ke dakonsu zuwa gabar da matasan suke. Suna budewa ciki kuwa sai suka tsinci kaji a jiki daskare da kankara. https://www.youtube.com/watch?v=tXugzAB8acA&pp=0gcJCdgAo7VqN5tD Me zaku ce?
Kalli Bidiyo: Baban Dan Bello ya taba zuwa sata a Kabari, tun daga nan ne ya bar garinsu na Galadanci ba’a sake jin duriyarsa ba saboda Abin Kunya>>Inji Murtala Gamji, Shugaban dattawan Matasan Najeriya wanda ya fito kare Shaikh Bala Lau

Kalli Bidiyo: Baban Dan Bello ya taba zuwa sata a Kabari, tun daga nan ne ya bar garinsu na Galadanci ba’a sake jin duriyarsa ba saboda Abin Kunya>>Inji Murtala Gamji, Shugaban dattawan Matasan Najeriya wanda ya fito kare Shaikh Bala Lau

Duk Labarai
Wani me suna Murtala Gamji, Shugaban dattawan Matasan Najeriya ya bayyana cewa ba zasu bari a rika taba malamai suna kyalewa ba. Ya bayyana hakane a wata bidiyo da kafar ATP Hausa ta wallafa. Ya kara da cewa, ko da fasto na garine aka ci zarafinsa ba zasu bari ya wulakanta ba zasu fito su kareshi. Da yake jawabi da kuma ikirarin baiwa Sheikh Bala Lau Kariya, ya kara da cewa, Dan Bello bashi da asali me kyau. Inda yace asalin mahaifinsa sata ya je yi a makabarta aka bishi, tun daga nan ne ya bar garinsu na Galadanci har yau bai dawo ba. Kalli Bidiyon a kasa: https://www.tiktok.com/@sultanjgn_backup/video/7489891789227265335?_t=ZM-8vJkufeYMUQ&_r=1 Me zaku ce?
Kalli Bidiyo:Yanda aka kama Wani Fasto wanda da ya gama wa’azi da rana a coci, sai ya koma da dare ya zama boka yana sihiri da sassan jikin mutane

Kalli Bidiyo:Yanda aka kama Wani Fasto wanda da ya gama wa’azi da rana a coci, sai ya koma da dare ya zama boka yana sihiri da sassan jikin mutane

Duk Labarai
Asirin Wani Fasto wanda asalinsa Boka ne dake sihiri da sassan jikin mutane ya tonu. Sunan Faston Onye Eze Jesus inda wasu jami'an tsaro da suka so kamashi suka je masa a matsayin wadanda ke son su yi kudi. Ya mince zai yi musu tsafi da sassan jikin mutum dan biyan bukatarsu. https://www.youtube.com/watch?v=jQWWp-mHe8w&pp=ygUVT255ZSBFemUgSmVzdXMgYXJyZXN0 An kamashine a jihar Anambra inda kuma ya amsa laifinsa.
Bayan da ya koma APC, shugaba Tinubu ya baiwa Sanata Shehu Sani mukamin Jakada

Bayan da ya koma APC, shugaba Tinubu ya baiwa Sanata Shehu Sani mukamin Jakada

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya fitar da sunayen mutanen da zai baiwa aikin jakadancin Najeriya zuwa kasashen waje. Tuni dai aka nemi wadanda sunayensu ya fita cewa su je ofishin DSS na kusa dasu dan a musu bincike kan tsaro sannan su bayar da bayanai kan ayyukan da suka taba yi a baya. Wata majiya me karfi ta bayyanawa jaridar Vanguard cewa akwai sunan Shehu Sani wanda bai dade da komawa jam'iyyar APC ba cikin wadanda aka baiwa mukamin sanatan. Sannan akwai tsaffin gwamnonin jihohin inyamurai watau Ifeanyi Ugwuanyi da Okezie Ikpeazu. Sannan majiyar tace akwai sunan Femi Fani Kayode sannan kuma akwai sunan Reno Omokri.
NDLEA Ta Cafke Shàķikai Biyu Dà Hodar Ìbĺìś Kilo 5 A Filin Jiŕgin Sàma Na Lagos Yayin Shirin Su Na Tafiya Zuwa Indiya

NDLEA Ta Cafke Shàķikai Biyu Dà Hodar Ìbĺìś Kilo 5 A Filin Jiŕgin Sàma Na Lagos Yayin Shirin Su Na Tafiya Zuwa Indiya

Duk Labarai
NDLEA Ta Cafke Shàķikai Biyu Dà Hodar Ìbĺìś Kilo 5 A Filin Jiŕgin Sàma Na Lagos Yayin Shirin Su Na Tafiya Zuwa Indiya Yayin da aka kama matashi ɗan birtaniya da kwayar loud filin jirgi; tsoho mai shekaru 75 da Skunk a Abia; tare da lalata fiye da kilo dubu 250 na tabar wiwi a Cross River Dakarun runduna ta musamman na Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa, wato NDLEA, sun kama wasu ‘yan uwan juna guda biyu: John Abugu mai shekaru 43 da Kenneth Abugu mai shekaru 31 a filin jirgin sama na Murtala Muhammed International Airport (MMIA) da ke Ikeja, Legas. An kama su da hodar Iblis mai nauyin kilo 5 da aka ɓoye a bangon jakunkuninsu, yayin da suke ƙoƙarin shiga jirgin sama zuwa kasar Indiya. An cafke su ne a ranar Alhamis 3 ga Afrilu, 2025, bayan samun sahihan bayanan si...