Buhari har yayi Mulkinsa ya gama bai kama kowa ba, kuma baisa a kama kowa ba>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad
Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana cewa Marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari bai kama kowa ba kuma bai sa a kama kowa ba har yayi mulkinsa ya gama.
Ya bayyana hakane a martanin da yakewa Dawisu, Watau Salihu Tanko Yakasai da yace Buhari ya kamashi.
Bashir yace idan dai Dawisu zai ce an kamashi a zamanin Mulkin Buhari zai yadda amma maganar cewa Buhari yasa an kamashi ba gaskiya bane.
https://twitter.com/BashirAhmaad/status/2001370109445562762?t=pvR-855gABYzJoFn1hwUeA&s=19








