Malamin Addinin Islama Sheikh Guruntum ya bayyana cewa, zaben shekarar 2027, kamar kwace kaine daga hannun azzalumai.
Malam dai bai yi karin haske ba amma yace yana fatan Angane karatun.
https://twitter.com/i/status/2009163897467752745
Wannan wani Dansandan kasar Ghana ne da ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta.
Dansandan ya taimakawa wani me motane da kudi suka kare masa kuma motarsa babu mai.
Dansandan ya bashi kudi kyauta
Hakan yasa ana ta yabawa dansandan saboda wannan abin kirki da yayi.
https://twitter.com/i/status/2009188457219043661
Wannan Dansandan Najeriyar ya dauki hankula bayan da aka ganshi ya kama wani me mota yana neman karbar cin hanci a hannunsa.
Me motar yace bashi da kudi a hannunsa amma yana da dubu biyar a account dinsa.
Dansandan ya cewa me motar su je POS a ciro kudin
Lamarin ya dauki hankula sosai.
Rahotanni daga jihar Rivers sun bayyana cewa, Majalisar Jihar ta fara shirin tsige gwamnan jihar, Simi Fubara.
An ga kakakin majalisar a wani Bidiyo daya watsu sosai a kafafen sada zumunta yana cewa 'yan majalisar 26 sun sakawa takardar neman tsige Fubara hannu.
https://twitter.com/i/status/2009198809163665530
Majalisar tace tana zargin Gwamna Fubara da karya dokar kundin tsarin Mulki.
Kuma sun ce zasu aika masa da takarda kan hakan.
Hakanan majalisar ta kuma ce ta fara shirin tsige mataimakin Gwamnan na jihar Rivers, Ngozi Nma Odu.
Majalisar ta kuma ce ta dakatar da shirin Gwamna Fubara na kai mata kasafin kudin shekarar 2026.
Wannan wani jirgin sama ne da ya rika kara kamar na tsohuwar mota yayin da ya zo tashi.
Daya daga cikin wadda suke cikin jirgin ce ta dauki Bidiyon inda tace sun tashi duk suna cikin tsoro.
https://twitter.com/i/status/2009154886727033026
A jiyane babbar kotun tarayya dake zaune a Abuja ta amincewa hukumar EFCC ta rike kadarori 57 mallakin tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami saboda ana zargin ya samesu ne ta hanyar da bata dace ba.
Ga Jadawalin Kadarorin kamar haka:
Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Washa kenan a wadanan hotunan inda take shakatawa a kasar waje.
Ta wallafa hotunan a shafinta na Instagram inda masoya da yawa suka yaba.
Wata matashiya daga Arewa da ta yi cikin shege ta haihu ta kuma mayar da dan inda ya fito ta dauki hankula.
Ta aikawa Malam tambaya ne inda tace ta tuba kuma tana neman yanda Allah zai yafe mata.
Abin dai ya baiwa mutane mamaki amma Malam yace idan da gaske ta tuba Allah zai yafe mata idan ta maye abinda ta aikata da kyakkyawa.
https://www.tiktok.com/@mhaliru92/video/7592682873547787541?_t=ZS-92tcnLlGekz&_r=1
Wannan wani ne da yace an kunna waqar Yabon Inyass a wani gidan giya dake kusa da su.
Ya walafa Bidiyon a shafinsa inda abin ya bashi mamaki.
https://www.tiktok.com/@abdullhd20/video/7592366405882891528?_t=ZS-92tav8zInqr&_r=1
Rahotanni sun bayyana cewa, Dangote ya janye zargin da yakewa shugaban Hukumar NMDPRA, Alhaji Farouk Ahmad a gaban Hukumar ICPC.
Dangoten ya janye zargin da yake wa Ahmad ne inda yace ya kashe dala Miliyan $7 wajan biyawa 'ya'yansa kudin makaranta a kasar Switzerland.
Wata Majiya tace Dangoten ya janye zarginne bayan da aka bukaci ya je da kansa ba aiken Lauya ba ya gabatar da hujjoji a gaban ICPC kan wannan zargin da yake.
Hakanan Wata Hujja da aka samu game da janye wannan korafi da Dangoten yayi shine EFCC ta fara bincike kan lamarin.
Saidai ICPC tace duk da wannan Janyewar da Dangote yayi ba zata yi watsi da binciken da takewa Ahmad ba, tace ta ma aika da bukatar bincike makarantar da ake zargin Ahmad din ya kai 'ya'yansa.
Ahmad dai tun tuni ya sauka daga kan mukaminsa ...