Monday, April 20
Shadow
Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Duk Labarai
Bankin (Afreximbank) ya bayyana cewa, Najeriya ce kasa ta 3 a jerin kasashen da suka fi yawan cin bashi a Africa. A wani bayani da ya fitar, bankin yace yawan ciyo bashi daga kasashen waje a tsakanin kasashen Adrica na ci gaba da karuwa. Yace hakan na faruwane saboda rashin ci gaban bangaren hada-hadar kudi na kasashen Afrikan. Bankin yace a watanni 6 na farkon shekarar 2024, kasashen Afrika 10 ne ke da kaso 69 na yawan bashin da aka ciwo a nahiyar. Kasashen sune South Africa (14%), Egypt (13%), Nigeria (8%), Morocco (6%), Mozambique (6%), Angola (5%), Kenya (4%), Ghana (4%), Côte d’Ivoire (3%), sai Senegal (3%). Bankin yace hakan na kara karuwane saboda yawan dogaron da kasashen ke yi da samun kudi ta hanyar neman tallafi daga kasashen yamma.
Da Duminsa: Kotu ta dakatar da Yunkurin ladaftar da sanata Natasha Akpoti da majalisa ke shirin yi

Da Duminsa: Kotu ta dakatar da Yunkurin ladaftar da sanata Natasha Akpoti da majalisa ke shirin yi

Duk Labarai
Babbar kotun tarayya dake Abuja ta dakatar da yunkurin ladaftar da Sanata Natasha Akpoti da majalisar tarayya ke shirin yi. Lauyoyin Sanata Natasha Akpoti ne suka shigar da kara inda suke neman kotun ta dakatar da kwamitin ladaftarwa dake neman tuhumar sanata Natasha Akpoti. Mai Shari'a Justice Obiora Egwuatu ya amince da wannan bukata inda yace an dakatar da wannan bincike. Yanzi dai majalisar ba zata iya ci gaba da binciken sana Natasha Akpoti ba har sai idan an samu daukaka kara ko wani sabon hukuncin ya fito.
A wannan shekarar kowa zai ga amfanin gyare-gyaren da gwamnatina ta yi, za’a ji dadi>>Gwamnatin Tinubu

A wannan shekarar kowa zai ga amfanin gyare-gyaren da gwamnatina ta yi, za’a ji dadi>>Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, a wannan shekarar da muke ciki ne za'a fara shaida romon gyare-gyaren da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu ta yi. Wasu daga cikin gyare-gyaren da Gwamnatin ta yi sun hada da cire tallafin man fetur, kara kudin wutar lantarki, kara kudin kira dana data, wanda wadannan abubuwa sun jefa 'yan Najeriya cikin matsi. Saidai da yake magana kan lamarin, Ministan yada labarai, Muhammad Idris ya bayyana cewa a wannan shekarar da muke ciki za'a fara ganin amfanin wadannan gyare-gyaren. Ya bayar da misali da kasafin kudin shekarar 2025 na Naira Tiriliyan 54.2 wanda yace tun da ake a kasarnan ba'a taba yin kamarsa ba. Yace wannan kasafin kudi an tsarashine dan kawowa 'yan Najeriya ci gaba da saukin rayuwa.
Babu wanda ya isa ya sauke Sanata Godswill Akpabio daga mukaminsa saboda wannan dan zargin da Natasha tai masa>>Inji Basaraken jihar Bayelsa

Babu wanda ya isa ya sauke Sanata Godswill Akpabio daga mukaminsa saboda wannan dan zargin da Natasha tai masa>>Inji Basaraken jihar Bayelsa

Duk Labarai
Basaraken jihar Bayelsa kuma shugaban sarakunan jihar, Bubaraye Dakolo Agada IV, ya bayyana cewa babu wanda ya isa ya sauke Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio. Ya bayyana cewa saboda wannan dan zargin da sanata Natasha Akpoti ta yi masa, bai isa ya sa a saukeshi ba. Yace su suna tare da Sanata Godswill Akpabio saboda dansu ne. Yace ya kamata awa Sanata Akpabio adalci kuma a kafa kwamitin bincikw da zai binciki lamarin. Yace Sanata Godswill Akpabio ya kawowa Najeriya ci gaba sosai.
‘Hotuna Da Duminsu: Yansanda sun harbawa masu zanga-zangar goyon bayan sanata Natasha Akpoti barkonon tsohuwa a Abuja

‘Hotuna Da Duminsu: Yansanda sun harbawa masu zanga-zangar goyon bayan sanata Natasha Akpoti barkonon tsohuwa a Abuja

Duk Labarai
Wasu mata sun fita yin zanga-zanga dan nuna goyon baya ga Sanata Natasha Akpoti data zargi kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio da neman yin lalata da ita. Masu zanga-zangar sun je kofar shiga majalisar tarayya ne suna suke yi zanga-zangar acan. Saidai tuni 'yansanda suka watsa musu barkonon tsohuwa inda suka watsa su. Hutudole ya fahimci cewa, masu zanga-zangar sun je kofar majalisar ne da misalin karfe 8 na safiyar yau, Laraba.
Tafiye-Tafiyen da Tinubu yayi sun kawowa Najeriya zuba jari na dala Biliyan $50

Tafiye-Tafiyen da Tinubu yayi sun kawowa Najeriya zuba jari na dala Biliyan $50

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya tace tafiye-Tafiyen da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke yi sun kawowa Najeriya zuba jarin dala Biliyan $50. Ministar masana'antu, Jumoke Oduwole ce ta bayyana hakan a wata ganawa da aka yi da ita ranar Talata a Abuja. Tace shugaban ya halarci taruka irin su na manyan kasashe mafiya karfin tattalin arzikin a Duniya watau G20 wanda kuma kamfanoni da yawa suka hadu a wajan. Tace wakilan wadannan kamfanoni da masu zuba jari sun kawo ziyara Najeriya kuma sun ga damar zuba jari kuma sun bayar da tabbacin zasu zo su zuba wannan jari a Najeriya.
Kai da kace idan ka zama shugaban kasa zaka halasta shan Wìwì shine kake da bakin cewa musulmai Jahilai? Kaine babban dakiki>>Reno Omokri ya mayarwa Sowore martani

Kai da kace idan ka zama shugaban kasa zaka halasta shan Wìwì shine kake da bakin cewa musulmai Jahilai? Kaine babban dakiki>>Reno Omokri ya mayarwa Sowore martani

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri ya mayarwa da dan takarar shugaban kasa, kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore martani kan zagin da yawa gwamnonin Arewa saboda sun bayar da hutun makaranta saboda zuwan watan Ramadan. Sowore yace Gwamnonin jihohin Kebbi, Katsina, Bauchi da kano dakikai ne kuma sakarkarune saboda sun bayar da hutun makaranta dalilin zuwan watan Azumin Ramadana. Inda ya bayar da hujjar cewa ko Saudi Arabia bata kulle makarantu saboda zu...