Thursday, March 26
Shadow
Kalli Bidiyon: A yi Hakuri, Abinda nake nufi shine ba zan baiwa wanda bashi da sana’a diyata ba>>Inji Ali Jita

Kalli Bidiyon: A yi Hakuri, Abinda nake nufi shine ba zan baiwa wanda bashi da sana’a diyata ba>>Inji Ali Jita

Duk Labarai
Tauraron Mawakin Arewa, Ali Isa Jita ya bayyana cewa, abinda yake nufi shine ba zai baiwa wanda bashi da sana'a diyarsa ba. Ya bayyana hakane a wani sabon Bidiyon daya wallafa bayan da Bidiyo na farko ya jawo cece-kuce inda aka rika ruwaito cewa yace ba zai baiwa Talaka diyarsa ba. Jita yace ko Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya nemi tsari daga Talauci. Yace kumama menene zai sa mutum ya ji cewa wai dashi ake da zarar an ce Talaka? Sannan yayi kira ga masu kafeshi shi da 'ya'yansa mata cewa hakan bai dace ba su daina dan ya sabawa doka. https://www.tiktok.com/@realalijita/video/7619402138174688532?_r=1&_t=ZS-94rpY0uzXWq&sp_source=7537614245375297080
Magance matsalar tsaro ba aikin Mutum daya bane, Nima Allah nake roko ya kawo mana zaman Lafiya>>Inji Shugaba Tinubu

Magance matsalar tsaro ba aikin Mutum daya bane, Nima Allah nake roko ya kawo mana zaman Lafiya>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo gida Najeriya daga kasar Ingila inda yaje ziyarar aiki. Shugaba Tinubu ya halarci Sallar Idi a jiya tare da mukarrabansa. A sanarwar da ya fitar ta taya Musulmai barka da sallah, shugaba Tinubu ya godewa Allah da ya sa aka gama Watan Ramadana Lafiya. Sannan ya jawo hankalin musulmai da su ci gaba da amfani da darasin da suka koya a wajan na Ramadana. Shugaba Tinubu ya kuma jawo hankalin cewa aikin tsaro bana mutum daya bane, inda yace mutane su rika bayar da hadin kai wajan kai rahoton duk wani abu da basu gane masa ba. Shugaban yace Shima kullun Allah yake roko ya kawo zaman lafiya, da ci gaba a Najeriya.
Kalli Bidiyon: Rainin Hankali ko tsokanar fada? Yanda wani Kirista yaje har Filin Idi yana karanta Baibul yana kira ga Musulmi su karbi kiristan

Kalli Bidiyon: Rainin Hankali ko tsokanar fada? Yanda wani Kirista yaje har Filin Idi yana karanta Baibul yana kira ga Musulmi su karbi kiristan

Duk Labarai
Wani Kirista ya je Filin Idi sanye da kaya irin na musulmai inda ya rika karanta Baibul yana kira ga musulmai su karbi kiristan. Saidai maimakon Musulman su nuna fishi, babu wanda ya masa komai. Asali ma har ya samu wasu musulmai ya rika zantawa dasu. https://twitter.com/i/status/2034919126192300231
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A yau Sallah, Daya daga cikin iyalin malam Nasiru Ahmad El-Rufai ta rigamu gidan gaskiya yayin da yake tsare a hannun ICPC

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A yau Sallah, Daya daga cikin iyalin malam Nasiru Ahmad El-Rufai ta rigamu gidan gaskiya yayin da yake tsare a hannun ICPC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, a yau Sallah, Matar Marigayi yaya a wajan tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, watau Bashir ElRufai, me suna Hajiya Safiya Ali Rufai ta rigamu gidan gaskiya. Ta rasu ne bayan gajeruwar rashin Lafiya. Dan tsohon Gwamnan, Hon. Bello ElRufai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X. Da fatan Allah ya jikanta. https://twitter.com/i/status/2034955729518367053