Friday, December 5
Shadow
Gwamna Dauda Lawal Dare ya baiwa Shugaba Tinubu sharadin sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro kamin ya koma APC

Gwamna Dauda Lawal Dare ya baiwa Shugaba Tinubu sharadin sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro kamin ya koma APC

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, Gwamnan jihar, Dauda Lawal Dare ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sharadin sauke Matawalle daga Ministan tsaro kamin ya yadda ya koma jam'iyyar APC. Jaridar Sunnews ta bayyana cewa, a baya gwamnan ya zauna da shugaban kasa Tinubu a Paris tare da gwamnonin Taraba da Enugu inda ya bayyana aniyarsa ta komawa APC. A yanzu da Muhammad Badaru Abubakar ya sauka daga ministan tsaro, Gwamna Dauda ya sake dawowa da bukatarsa inda yace a sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro shi kuma zai koma APC. Yayi Alwashin jawo mutane da yawa mabiyansa zuwa jam'iyyar ta APC a jihar Zamfara.
Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Dambarwa ta barke a majalisa inda wasu sanatoci suka ce a bar Janar Christopher Musa ya wuce amma wasu sukace basu yadda ba sai an masa tambayoyin da suka kamata

Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Dambarwa ta barke a majalisa inda wasu sanatoci suka ce a bar Janar Christopher Musa ya wuce amma wasu sukace basu yadda ba sai an masa tambayoyin da suka kamata

Duk Labarai
An samu dambarwa a majalisar Dattijai yayin tantance janar Christopher Musa a matsayin Ministan tsaro. Sanata Sani Musa daga jihar Naija ya nemi a bar Janar Christopher Musa ya wuce kamar yanda aka sabawa ministocin da aka aika majalisar dan a tantancesu. Yace Janar Musa tsohon sojane sannan kuma duk tambayoyin da suke masa yanzu sun taba masa irinsu a baya dan haka shi a shawarce yana ganin a kyaleshi ya wuce kawai. Saidai bai samu goyon bayan sauran 'yan majalisar ba inda suka ce ya kamata a tsaya a masa tambayoyin da suka kamata. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1996240738586153221?t=RWLtj3y8T64C4iwGVKBp6g&s=19
Mun Baka Wata 6 idan baka tabuka abin azo a gani ba, zamu sa a tsigeka>>Majalisar Tarayya ta gayawa Janar Christopher Musa

Mun Baka Wata 6 idan baka tabuka abin azo a gani ba, zamu sa a tsigeka>>Majalisar Tarayya ta gayawa Janar Christopher Musa

Duk Labarai
Sanatoci a majalisar Dattijai sun bayyanawa janar Christopher Musa cewa, sun bashi watanni 6 su ga kokarinshi a wajan magamce matsalar tsaro. Sun ce idan bai tabuka komai ba har watanni 6 suka wuce to lallai zasu bada shawarar a tsigeshi a matsayin Ministan tsaro. Sun bayyana hakane yayin tantance shi a zauren majalisar. https://twitter.com/thecableng/status/1996234023127965814?t=i8Ff53GnNIU2bHJ1A3gfVw&s=19
Burin kowane Tshàgyèràn Dhàjì dake kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda a tunaninsu Najeriya akwai kudi>>Inji Janar Christopher Musa

Burin kowane Tshàgyèràn Dhàjì dake kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda a tunaninsu Najeriya akwai kudi>>Inji Janar Christopher Musa

Duk Labarai
Janar Christopher Musa ya bayyana cewa, Burin kowane dan Bindiga a kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda tunaninsu a Najeriya akwai kudi. Ya bayyana hakane a lokacin tantancesa a majalisar Dattijai. Ya kara da cewa zai hada kai da sauran ma'aikatun tarayya da kuma jami'an tsaro da kasashe makwabtan Najeriya da dauransu dan samar da tsaro. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1996228876444340649?t=mUwYTwatPHCs2AXDYSIgcg&s=19
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya raba motocin yakin neman zaben 2027 ga duka jihohin Najeriya

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya raba motocin yakin neman zaben 2027 ga duka jihohin Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya raba motocin yakin neman zaben 2027 ga masu shirya yi masa yakin neman zaben 2025. Rahoton daga Sahara reporters yace shugaba Tinubu ya nada gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma a matsayin wanda zai jagoranci wannan tafiya. Sannan an bukaci kowace jiha ta samar da Naira Biliyan 1 dan nasarar wannan tafiya kamar yanda rahoton ya nunar. Hakan na zuwane yayin da ake fama da matsalar tsaro a Najeriya
Da Duminsa: Yanzu Haka Janar Christopher Musa ya jisa Majalisar  Dattijai dan a tantanceshi a matsayin Ministan tsaro

Da Duminsa: Yanzu Haka Janar Christopher Musa ya jisa Majalisar Dattijai dan a tantanceshi a matsayin Ministan tsaro

Duk Labarai
Rahotanni daga Abuja na cewa, Janar Christopher Musa ya isa majalisar Dattijai dan a tantanceshi a matsayin Ministan tsaro https://twitter.com/channelstv/status/1996205376778453341?t=nsyc5Yb0xLfouUFRkH4nUg&s=19 A jiyane shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikewa da majalisar Dattijai da sunan Janar Christopher Musa dan ta tantanceshi.
Da Duminsa: Hadiza Gabon Ta yi Martani me zafi ga masoya Adam A. Zango masu sukarta kan cewa bata saka hoton Adamun ba a gyaran datawa dakin da take hira da mutane ba

Da Duminsa: Hadiza Gabon Ta yi Martani me zafi ga masoya Adam A. Zango masu sukarta kan cewa bata saka hoton Adamun ba a gyaran datawa dakin da take hira da mutane ba

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon tawa Masoya Adam A. Zango martani me zafi kan sukar da suke mata ta cewa bata saka hoton Adam A. Zango a dakin da take hira da mutane ba a ciki. A baya Hutudole ya kawo muku irin yanda masoya Adam A. Zango ke tawa Hadiza Gabon martani da kiranta da sunaye daban-daban kan wannan abu. Saidai a martaninta, Hadiza Gabon tace Na dauka idan mutum ya gina gida zai iya masa kalar Fentin da yake so. Hakan na nuna cewa, Gabon tana sane da abinda ta yi ba kuskure bane.
Fàdàn cacar Baki ya barke tsakanin Hausawa Musulmai ‘yan Arewa da Inyamurai a kafafen sada zumunta inda Hausawa suka fara mayar da martani kan shaguben da akewa ‘yan Arewa na cewa Inyamurai su koyi Hausa saboda ko da Tshàgyèràn Dhàjì sun kamasu

Fàdàn cacar Baki ya barke tsakanin Hausawa Musulmai ‘yan Arewa da Inyamurai a kafafen sada zumunta inda Hausawa suka fara mayar da martani kan shaguben da akewa ‘yan Arewa na cewa Inyamurai su koyi Hausa saboda ko da Tshàgyèràn Dhàjì sun kamasu

Duk Labarai
A baya hutudole ya kawo muku rahoton cewa, Inyamurai na koyon Hausa wai da tunanin idan 'yan Bindiga suka kamasu suka musu Hausa, zasu sakesu. Duk da yake abin ya zama kamar barkwanci amma da yawan Hausawa sun daukeshi a matsayj cin fuska da tsangwama da nuna cewa 'yan Bindiga masu garkuwa da mutane ana musu kallon Hausawa ne. Wannan dalili yasa Hausawa daga Arewa suma suka kafara mayar da martani ta hanyar dora wakokin Inyamurai suna bi a kafafen sada zumunta suna cewa idan masu son kafa kasar Biafra sun kamaka, kana yi musu wannan taken shikenan. Wasu kuma sun rika cewa wai masu tsafi da iyayensu sune suke zagin Hausawa? Hakan yasa suma Inyamuran abin bai musu dadi ba inda suka fara mayar da martani. Kalli Bidiyon a comment: https://www.tiktok.com/@surajrukky/video/75...
Kaso 80 na Tshàgyèràn Dhàjì Hausawa ne daga Arewa>>Inji VDM

Kaso 80 na Tshàgyèràn Dhàjì Hausawa ne daga Arewa>>Inji VDM

Duk Labarai
Tauraron kafafen sada zumunta kuma wanda ke ikirarin fafutuka, VDM ya bayyana cewa kaso 80 na 'yan Bindiga masu yaren Hausa ne daga Arewacin Najeriya. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya yadu sosai a kafafen sada zumunta inda ciki hadda 'yan uwansa 'yan Kudu da yawa sun mayar masa da raddi. https://www.tiktok.com/@lordashore/video/7579335248035564822?_t=ZS-91ugGhJeNTU&_r=1